Tuesday, January 31, 2017

Malaman Makarantun ‘Foli’ sun shiga yajin aiki



Kungiyar ASUP tace babu wani ja da baya a kokarin ta na shiga yajin aiki


Gwamnatin tarayya dai tayi kokarin a sasanta amma abin ya ci tura


Sai dai wasu Makarantun sun ki shiga yajin aikin






Mr. Anderson Ezeibe, wanda shine Sakataren Kungiyar ASUP ta Malaman Makarantun Polythechnic yace sun tafi yajin aiki na mako daya kuma babu maganar ja da baya a kan batun na su.

Malaman Makarantun na gaba da Sakandare sun tafi yajin aikin ne a tsakar daren jiya bayan duk wani yunkuri sasanci da Gwamnati ya ci tura. Kungiyar tace kaf ma’aikatan na ta za su janye aiki har sai wa’adin ya kare.




Kungiyar za ta tafi yajin aikin mako guda ne a matsayin gargadi kafin idan abubuwa sun dace su dawo, idan kuma ba haka ba to sai baba ta gani. Tun bara dai Kungiyar ta ke kukan za ta tafi yajin aiki, sai dai Kungiyar tace Gwamnati ba tayi komai ba.

Kungiyar tace kowace Makaranta tana cikin yajin, to sai dai ga shi Makarantar Polythechnic ta Jihar Kaduna ba ta bi sahu ba.


[NAIJ Hausa]

No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...