– Gwamnan
Jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufa’i ya nuna ba da wasa yake ba
– Gwamnan
yace duk Kwamishinan da ba zai iya ba, ya sauka
– El-Rufa’i
ya shirya kammala duk wasu manyan ayyuka a wannan shekarar
Mai girma Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir Ahmed El-Rufa’i
ya nuna ba fa wasa ya fito yi ba. Gwamnan yayi kira ga mukarraban sa yace duk
wanda ba zai iya ba ya ba shi wuri. Gwamnan yayi wannan jawabi ne a zaman da
Gwamnatin Jihar tayi na dabbaga ayyukan wannan shekarar.
Mai Girma Gwamnan ya sha alwashin kammala duk wasu manyan
ayyuka da ya dauko a wannan shekarar, ya bayyyana haka ne a wannan taron da
Gwamnatin Jihar da Ma’aikatar kasafin kudi su ka hada na kwanaki 2 a jere.
Gwamnan ya duba ayyuka da kuren da suka yi a shekarar da ta wuce da niyyar a
gyara su wannan shekara.
Gwamna El-Rufa’i yace daga yanzu dole kowace Ma’aikata ta
rika kirkiro manyan ayyukan gina Jiha, ya kuma bada umarni kowane Kwamishina ya
rika fita yana duba ayyukan da Jiha ta ke yi. Gwamnan yace daga yanzu zama
cikin Ofis ya karewa Kwamishinoni.
Malam Nasiru dai yace duk Ma’aikatar da ba ta kawo kudi,
ba za ta ga kudi ba a kwaryar ta. Don haka ne ma Gwamnan yace duk Kwamishinan
da ba zai iya tatso akalla Miliyan 10 a wata ba ya tafi gida. Gwamnatin dai
tana da kwanaki kusan 850 ta cika alkawuran da ta dauka Inji Kwamishina Muhammad Sani Dattijo.
[NAIJ Hausa]
No comments:
Post a Comment