Sunday, January 29, 2017

Mutumin da ya auri mata kusan 100 ya mutu



Mai mata 100 ya mutu; yayi wasiyya a daina zina



Bello Abubakar Masaba, mutumin da ya auri mata barkatai ya riga mu gidan gaskiya


Bello Masaba ya mutu yana da mata kusan 100


– Bello Masaba ya rasu yana da shekaru 93




Idan ba a manta ba akwai wani ta’aliki mai suna Bello Abubakar Masaba, wani mutumin Bida ta Jihar Neja mai mata barkatai. Wannan mutumi dai yanzu Allah yayi masa cikawa a jiya Asabar bayan yayi ‘yar gajerar rashin lafiya.

Masaba dai ya yanke jinki ya fadi har sau biyu, daga karshen yace ga garin ku. Wata Jarida mai suna The Eagle ta bada labarin rasuwar wannan mutumi. Alhaji Mutairu Salahuddeen; wani mai magana a madadin dangin wannan mutumi ya tabbatar da haka.





Bello Masaba dai kowa ya san sa da yawan mata, ace mai mata 97, yayi mata kusan guda 107, ya kuma rasu ya bar fiye da 80, bayan ya rabu da wasu da dama. Ya haifi ‘ya ‘ya sama da 185, sai dai wasu sun rasu, yanzu ya bar akalla guda 133.

Bello Masaba dai ya rasu ne jiya da rana, an kuma shirya jana’izar sa a Ranar yau da safe. Marigayin yayi wasiyya da a daina zinace-zinace a koma auren mata na addini. Masaba ya mutu yana da shekaru 93.


[NAIJ Hausa]

No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...