Mai
mata 100 ya mutu; yayi wasiyya a daina zina
– Bello
Abubakar Masaba, mutumin da ya auri mata barkatai ya riga mu gidan gaskiya
– Bello Masaba ya mutu yana da mata kusan 100
– Bello Masaba ya rasu yana da shekaru 93
Idan ba a manta ba akwai
wani ta’aliki mai suna Bello Abubakar Masaba, wani mutumin Bida ta Jihar Neja
mai mata barkatai. Wannan mutumi dai yanzu Allah yayi masa cikawa a jiya Asabar
bayan yayi ‘yar gajerar rashin lafiya.
Masaba dai ya yanke jinki ya
fadi har sau biyu, daga karshen yace ga garin ku. Wata Jarida mai suna The Eagle ta bada labarin rasuwar wannan
mutumi. Alhaji Mutairu Salahuddeen; wani mai magana a madadin dangin wannan mutumi ya
tabbatar da haka.
Bello Masaba dai kowa ya san
sa da yawan mata, ace mai mata 97, yayi mata kusan guda 107, ya kuma rasu ya
bar fiye da 80, bayan ya rabu da wasu da dama. Ya haifi ‘ya ‘ya sama da 185,
sai dai wasu sun rasu, yanzu ya bar akalla guda 133.
Bello Masaba dai ya rasu ne
jiya da rana, an kuma shirya jana’izar sa a Ranar yau da safe. Marigayin yayi
wasiyya da a daina zinace-zinace a koma auren mata na addini. Masaba ya mutu
yana da shekaru 93.
No comments:
Post a Comment