Jami’ar
KASU: An nada sabon Shugaba
– Jami’ar KASU ta Kaduna ta nada sabon Shugaba
– Farfesa Mohammed Tanko ne sabon Shugaban Jami’ar
– Gwamnan
Jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufa’i ya tabbatar da nadin
A jiya ne Gwamnan Jihar
Kaduna, Mai Girma Malam Nasir Ahmed El-Rufa’i ya tabbatar da nadin Farfesa
Mohammed Tanko a matsayin Shugaban Jami’ar ta Jihar Kaduna watau KASU. Wannan
ya biyo bayan mataki da Hukumar kula da Jami’ar ta dauka
Farfesa Tanko dai Malamin
Jami’ar ne tun asalin sa, ya rike Shugaban sashe da Tsangayan Tattali na
Makarantar da kuma Mataimakin Shugaban Jami’ar a baya. Kai bari ma dai ya taba
rike Mukaddashn Shugaban Jami’ar a wani karo, don haka ya san harkar Jami’ar
ciki-da-bai.
An haifi Mohammed Tanko ne a
Kawo, Farfesa ne a bangaren akawu. Tanko yayi Digirin san a farko a Jami’ar
Bayero ta Kano a fannin Ilmin akawu, daga nan yayi digirgir da kuma MBA a
shekarar 2000. A shekarar 2005 Tanko ya kammala karatun Digiri na uku a Jami’ar
ABU Zaria.
Farfesa Tanko kwararren
Akawu ne, ya kuma rike matsayi da dama har a Gwamnatin Jihar Kaduna, ya kuma
yaye dalibai masu karatun Digiri da dama. Yana da rubuce-rubuce masu yawan
gaske.
[NAIJ Hausa]
No comments:
Post a Comment