Wednesday, January 25, 2017

Sanata Shehu Sani ya karyata Fadar Shugaban Kasa


Sanata Shehu Sani yace sam ba Shugaba Buhari ya rubuta wasikar da ta wanke Babachir ba


A wasikar da aka maido wa Sanatocin martani jiya, shugaban kasa ya wanke Babachir Lawal


Shehu Sani yace an yi jana’izar yaki da rashawa




Sanata Shehu Sani mai wakiltar Yankin tsakiyar Kaduna yayi tir tare da mamaki ga martanin wasikar da aka samu daga fadar Shugaban kasa inda aka wanke Sakataren Gwamnatin Tarayya, Babachir David Lawal daga dukkan zargi.

Shehu Sani yace Fadar Shugaban Kasa tayi karya a wasikar ta, Sanatan yace ba shakka sun gayyaci Sakataren Gwamnatin domin ya kare kan sa a Majalisar. Haka kuma Sanatan da ya gudanar da bincike game da Sakataren yace kusan ‘yan kwamitin na sa, sun sa hannu a takardar da ya gabatar ba kamar yadda wasikar Shugaban Kasa ta fada ba.


Shehu Sani dai yayi mamakin yadda Fadar Shugaban Kasa tayi mursisi ta hau kujerar naki game da rokon da aka yi na tsige Sakataren Gwamnati, Babachir David Lawal bisa zargin mikawa Kamfanin sa wasu kwangila.

Shehu Sani yace yanzu an yi jana’izar yaki da cin hanci da rashawa a Gwamnatin Shugaba Buhari. Don kuwa ana tsince wadanda za a bincika ne da laifi a Mulkin na Buhari.



[NAIJ Hausa]

No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...