Sunday, January 22, 2017

Ku kashe Fulani, ku yanka masu wuya-Inji wani Fasto



– Fasto Sulaiman yayi kira ga Mabiyan sa da su kashe Makiyaya Fulani


– Faston yace duk Makiyayin da aka gani kusa da Cocin sa a aika sa Lahira


– Wannan kalaman dai suna iya kawo rikici a Kasa






Wani Fasto mai suna Johnson Sulaiman ya ba Mabiyan sa umarnin kashe duk wani Makiyayi da aka gani kusa da Cocin sa. Babban Faston na Omega Fire yace idan har aka ga wani Fulani-Makiyayi kusa da cocin sa, a aika sa Lahira kurum.

Faston yace Makiyaya Fulanin suna neman kai masa hari su ga bayan sa. Yanzu haka dai bidiyon na ta yawo a yanar gizo, ko da yake ba a san yaushe ne Faston ya fadi wannan maganar ba, amma dai da alamu cikin ‘yan kwanakin nan ne.

Faston dai yace Fulani Makiyaya suna kokarin tada fitina a Cocin na sa, yace don haka ne wani ya kira sa ya fada masa domin ya dauki mataki. Don haka ne dai ya sanar da Mabiyan sa cewa ka da a ragawa wani duk Makiyayi da aka gani a kusa da wurin bautar na su.

Faston yace ko da wasa wani Makiyayi ya shigo a yanka wuyan sa, a kashe shi, kuma babu abin da zai faru. Wannan kalamai dai suna iya tada rikici. 


[NAIJ Hausa] 






No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...