Tuesday, January 31, 2017

An bankado wani laifin su Saraki da Dogara



Ta kwabe da Shugabannin Majalisar Kasar nan a halin yanzu


– Wata Kungiya ta bankado barnar da su Saraki suka yi da sunan gidajen haya


Ana zargin Bukola Saraki da Yakubu Dogara da Mataimakan sa da yin sama da wasu Miliyan 600






Ana zargin Shugabannin Majalisar Kasar nan da yin gaba da wasu kudi sama da Naira Miliyan 600. Kamar dai yadda Sahara Reporters ta fada akwai hannun shi Bukola Saraki da Mataimakin sa; Ike Ekeremadu da kuma Yakubu Dogara da na sa Mataimakin; Yusuf Lasun.

Wata Kungiya mai suna CATBAN ce ta zargi Shugabannin Majalisar Dattawa da Wakilan Tarayyar Kasar da matsawa Hukumar FCDA mai kula da harkokin Birnin-Tarayya Abuja har sai da aka ba su gidajen kwana bayan kuma Gwamnati ta basu kudin gida.

Hukumar ta FCDA mai kula da cigaban Birnin-Tarayyar tace dai ta kashe kudi har N630,125,499.90 domin kamawa manyan ‘Yan Majalisar haya da kuma gyaran gidajen da aka kaman. Sai dai ashe ‘Yan Majalisun suna zaune cikin gidajen su na kan su ne, sai suka karkatar da kudin da aka ware na hayan su saka a aljihu abin su.


[NAIJ Hausa]

No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...