– Ta
kwabe da Shugabannin Majalisar Kasar nan a halin yanzu
– Wata Kungiya ta bankado barnar da su Saraki suka yi da sunan gidajen haya
– Ana
zargin Bukola Saraki da Yakubu Dogara da Mataimakan sa da yin sama da wasu
Miliyan 600
Ana zargin Shugabannin Majalisar Kasar nan da yin gaba da
wasu kudi sama da Naira Miliyan 600. Kamar dai yadda Sahara Reporters ta fada
akwai hannun shi Bukola Saraki da Mataimakin sa; Ike Ekeremadu da kuma Yakubu
Dogara da na sa Mataimakin; Yusuf Lasun.
Wata Kungiya mai suna CATBAN ce ta zargi Shugabannin
Majalisar Dattawa da Wakilan Tarayyar Kasar da matsawa Hukumar FCDA mai kula da
harkokin Birnin-Tarayya Abuja har sai da aka ba su gidajen kwana bayan kuma
Gwamnati ta basu kudin gida.
Hukumar ta FCDA mai kula da cigaban Birnin-Tarayyar tace
dai ta kashe kudi har N630,125,499.90 domin kamawa manyan
‘Yan Majalisar haya da kuma gyaran gidajen da aka kaman. Sai dai ashe ‘Yan
Majalisun suna zaune cikin gidajen su na kan su ne, sai suka karkatar da kudin
da aka ware na hayan su saka a aljihu abin su.
[NAIJ Hausa]
No comments:
Post a Comment