Monday, January 9, 2017

Hisbah ta fasa kwalabe fiye da 1000 na giya



– Jami’an Hisbah sun fasa kwalaben giya a Kano fiye da 1000


Wannan a shekarar da ta gabata kurum kenan


Dokar shari’a ta haramta shigo da giya


Jami’an Hisbah a Kano sun fasa kwalabe sama da 1000 na giya a Jihar Kano da a ka kama shekarar da ta wuce. Darektan Hukumar Hisbah ta Jihar mai kula da harkokin Addinin Musulunci ya bayyana haka ga manema labarai.

Abba Sufi yace Ma’aikatan Karamar Hukumar Dawakin Kudu suka yi wannan aiki a Ranar Talatan da ta wuce. An dai kona kwalaban ne a gaban Ma’aikatan Hukumar da sauran Jama’a. An karbe kwalaban giyan ne bayan an bada hukunci a Kotu.

A Jihar Kano dai ana amfani da dokar shari’ar Musulunci wanda ta hana shigowa ko shan kayan barasa. Ma’aikatan Hisbah kuma za su kara kokari wajen ganin an bi wannan doka a fadin Jihar a wannan shekarar da aka shiga.

A bangaren siyasa kuwa, ‘Yan Kwankwasiyya a Jihar Kano sun yi kokarin gudanar da wani taro a Ranar Litinin din wannan makon, sai dai abin bai yiwu ba, bayan da aka turo ‘Yan Sanda suka zagaye wajen taron. Jaridar Daily Trust dai ta bada labarin abin da ya faru.




[NAIJ Hausa]

No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...