Thursday, January 19, 2017

Barayin shanu sun tuba a Jihar Katsina


Gwamnatin Jihar Katsina ta bada lamuni ga barayin dabbobi


Tsofaffin barayin shanun da dama sun mika wuya, sun ajiye makamai


An maido bindigogi da dabbobi da dama




Gwamnatin Jihar Katsina ta bada lamuni ga barayin dabbobi a Yankin. Hakan ta sa da dama sun ajiye makaman su ga hukuma. An dai samu bindigogi fiye da 300 da kuma dabbobi masu yawan gaske.

Bayanai sun nuna cewa an samu maido dabbobi sama da 28,000 da aka sata a baya. An dai kuma samu bindogin AK har guda 97 da kuma sauran kananan bindigogi fiye da 200. Daruruwan mutane ne dai suka mika wuya suka ajiye makaman na su yayin da Gwamnati ta bada lamuni.




Sakataren Gwamnatin, Dr. Mustafa Inuwa ya bayyana haka a Garin Kankara idan aka mika makaman. Wannan dai yana cikin kokarin Gwamnatin na kawo karshen rikicin makiyaya da manoma. Tuni dai an mika mafi yawan dabbobin da aka maido ga masu su.

A Kaduna kuma, Dan Majalisar da ke wakiltar Karamar Hukumar Kaura da ke cikin Kudancin Jihar, Honarabul Gideon Gwani ya koka da yadda lamarin tsaro ya tabarbare a Yankin. Dan Majalisar yace Mutanen suna cikin matsala dare da rana.

                       
[NAIJ Hausa]

No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...