– Kungiyar ‘Yan Jarida na Kasa ta
soke rajistar Jaridar Al-Mizan
– NUJ tace tayi kuskure wajen
rajistar Jaridar
– Jaridar Al-Mizan ta ‘Yan Shi’a ce
Kungiyar
NUJ ta ‘Yan Jaridun Najeriya ta soke rajistar Jaridar nan ta Al-Mizan. Wannan
mataki dai ya zo ba da bata wani lokaci ba kamar yadda Kungiyar ta bayyana
bayan wani taron da tayi a karshen makon da ya wuce.
Sakataren
Bangaren Kungiyar na Jihar Kaduna, Dauda Idris Doka ya sa hannu wajen matakin
da aka dauka. Kungiyar ta bayyana cewa ta gano Jaridar ta ‘Yan Shi’a ce a zaman
ta da tayi na zartarwa a Ranar 29 ga watan nan.
Kungiyar
ta NUJ dai tace ba ruwan ta da wani addini, asali ma dai tana kokarin kare duk
wasu Addinai da kuma Kabilu na Kasar ne. Kungiyar don haka tace tayi kusukuren
ba Jaridar Al-Mizan lasisi a baya. Daga yanzu dai bai hallata Jaridar ta ci gaba da aiki ba.
Jaridar
Al-Mizan din da kuma ta Turancin ta watau Pointer Express ta Kungiyar IMN ce ta
Shi’a. A baya dai NUJ ta hana Jaridu da dama lasisi saboda wannan dalilai.
[NAIJ Hausa]
No comments:
Post a Comment