– A Jihar Kwara, Ma’aikata sun
komawa Azumi da Salla bayan an yi wata da watanni babu albashi
– Gwamnatin Kwara dai ta kwashi
watanni 6 ba ta biya Ma’aikata albashi ba
Yanzu haka a Garin Ilorin,
Malaman Makaranta da dama sun koma azumi inda suke rokon Ubangiji ko a samu a
biya su albashin sun a wata-da-watanni. Ma’aikatan Makaranta na bin Gwamnatin
Jihar Kwara dai bashin albashi har na watanni 6.
Mataimakin Shugaban Kungiyar
Malamai watau NUT ya bayyana haka a Ranar Litinin. Alhaji Salihu Toyin wanda
shine kuma Shugaban wata Makaranta a Ilorin yace yanzu kuma sun koma hannun
Ubangiji ko albashin su zai fito.
Jaridar Vanguard tace, Yanzu
dai Malaman Makaratun Jihar za su shiga azumi da rokon Ubangiji da Musulman su
da Kirista domin su samu kudin su. Gwamnati dai ta fara biyan wasu albashin,
amma har yanzu Ma’aikatan na bin bashin wasu kudin. Malaman Makarantun Kwara
dai suna shan wahala matuka.
No comments:
Post a Comment