Sunday, January 29, 2017

Ina na kan baka na, Inji Faston da yace a kashe Fulani


– Fasto Johnson Sulaiman yayi kira ga Mabiyan sa da su kashe Makiyaya Fulani kwanakin baya


– Faston yace duk Makiyayin da aka gani kusa da Cocin sa a aika sa Lahira


– Har yanzu dai yace ba zai nemi gafarar abin da ya fada ba


– Fasto Johnson yace ba fada yake da Hausa/Fulani ba




Fasto Johnson Sulaiman na cocin na Omega Fire ya ba Mabiyan sa umarnin kashe duk wani Makiyayi da aka gani kusa da Cocin sa. Faston yace a yanka masu wuya nan take, sai dai wadannan kalamai sun nemi su tada Kasar.

Faston yace ba zai nemi gafarar kowa ba, Faston ya fadi haka ne a wata huduba da yayi wa Mabiyan na sa. Faston dai yace ba fada yake da Fulani ko Hausawa ba, ya kira su mutanen kirki masu matukar hakuri.

Shi dai Faston yace idan har aka ga wani Bafullatani ya shigo cikin cocin na sa ko da wasa ne a aika sa lahira. Faston yace don kuwa Fulani suna kashe Kiristoci a fadin Kasar babu abin da kuma aka yi, don haka su ma za su yi hakan.

Hukumar DSS dai ta nemi ta cafke Fasto Sulaiman bayan yayi wannan kalamai, Gwamna Fayose na Ekiti yayi wuf ya je ya hana. Tun bayan nan ne kuma Gwamna Fayose ya zama Direban Faston.


[NAIJ Hausa]





No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...