– Fasto Johnson Sulaiman yayi kira
ga Mabiyan sa da su kashe Makiyaya Fulani kwanakin baya
– Faston yace duk Makiyayin da
aka gani kusa da Cocin sa a aika sa Lahira
– Har yanzu dai yace ba zai nemi
gafarar abin da ya fada ba
– Fasto Johnson yace ba fada yake da Hausa/Fulani ba
Fasto
Johnson Sulaiman na cocin na Omega Fire ya ba Mabiyan sa umarnin kashe duk wani
Makiyayi da aka gani kusa da Cocin sa. Faston yace a yanka masu wuya nan take,
sai dai wadannan kalamai sun nemi su tada Kasar.
Faston
yace ba zai nemi gafarar kowa ba, Faston ya fadi haka ne a wata huduba da yayi
wa Mabiyan na sa. Faston dai yace ba fada yake da Fulani ko Hausawa ba, ya kira
su mutanen kirki masu matukar hakuri.
Shi
dai Faston yace idan har aka ga wani Bafullatani ya shigo cikin cocin na sa ko
da wasa ne a aika sa lahira. Faston yace don kuwa Fulani suna kashe Kiristoci a
fadin Kasar babu abin da kuma aka yi, don haka su ma za su yi hakan.
Hukumar
DSS dai ta nemi ta cafke Fasto Sulaiman bayan yayi wannan kalamai, Gwamna
Fayose na Ekiti yayi wuf ya je ya hana. Tun bayan nan ne kuma Gwamna Fayose ya
zama Direban Faston.
[NAIJ Hausa]
No comments:
Post a Comment