Monday, January 23, 2017

Fayose ba shi da hankali Inji Sanata Kashamu


Bai dace Ayo Fayose ya jagoranci PDP ba-Inji Sanata Kashamu




– Sanata Buruji Kashamu yayi raga-raga da Gwamna Ayo Fayose na Jihar Ekiti


– Sanatan yace bai dace a nada Ayo Fayose a matsayin Shugaban Gwamnonin PDP ba


 – Makon jiya aka nada Gwamna Fayose a matsayin Shugaban Gwamonin PDP na Kasar


Sanata Buruji Kashamu yayi tir da shawarar da Jam’iyyar PDP ta dauka na nada Gwamna Ayodele Fayose na Jihar Ekiti a matsayin shugaban Gwamnonin Jam’iyyar PDP. Fayose dai ya canji Gwamna Mimiko wanda wa’adin sa na daf da karewa.

Buruji Kashamu Sanata mai wakiltar Gabashin Ogun yace ko kadan Fayose bai dace da rikon wannan shugabanci ba. Kashamu yace hayaniya kurum ya cika kan na Fayose, babu ilmin komai. Kashamu ya kara da cewa Fayose yak an yi abubuwa kamar karamin yaro, yace da irin su aka nada a wannan matsayi.

Buruji Kashamu yace ya kamata ‘Yan PDP su nuna rashin amincewar su da wannan mataki da aka dauka. Kashamu yace babu abin da Fayose zai yi illa ya kashe Jam’iyyar PDP gaba daya don kuwa babu wanda zai yi aiki da shi.




[NAIJ Hausa]

No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...