Wanene
sabon shugaban kasar Ghana Nana Akufo-Addo?
– An
rantsar da Nana Akufo-Addo a matsayin sabon shugaban kasar Ghana jiya
– Kamar Buhari, Nana ya doke Shugaba John Mahama daga
kujerar sa bayan ya dade yana neman takara
– Shin wai wanene ma Nana Akufo-Addo?
A Jiya 7 ga wannan watan ne
aka rantsar da Nana Akufo-Addo a matsayin sabon shugaban Kasar Ghana. Nana
Akufo-Addo ya doke shugaban kasa John Dramani Mahama daga kan kujerar sa a
zaben da aka gudanar a watan Disamban bara kamar dai yadda Shugaba Buhari yayi da Jonathan Goodluck. Shugaba Buhari kuma ya kifar da Shagari ne a watan Disamban 1983.
Shin wai wanene sabon
shugaban kasar? Wanda ya shigo da wayar salula cikin Ghana?
An dai haifi Nana a tsakiyar
Accra, shekaru 72 da suka wuce. Watau dai kamar Shugaba Buhari na Najeriya, ya karbi mulki yana shekaru fiye da 70. Mahaifin sa, Edward Akufo-Addo yana cikin
Alkalan farko na Kasar ya kuma rike shugabancin Kasar daga shekarar 1969 zuwa
1972. Sai dai shi Buhari ne ya rike Shugabanci a baya ba uban sa ba.
Nana dai yayi karatu a Gida da kuma Kasar Ingila. Haka ma kuwa Shugaba Buhari na Najeriya ya leka Kasashe irin su Amurka. A shekarar 1975 ya shiga
Kotu bayan ya karanci Ilmin tattali da kuma shari’a a Ingila. Yayi aiki a
wurare da dama har da Amurka.
Akwai ma dai lokacin da ya rike Ministan shari’a
na Kasar Ghana. Addo dai tun yana shekara 30 a Duniya yake siyasa. Haka Shugaba Buhari ya rike Gwamna da ma Minista, kuma tun yana matashi ya sha kifar da Gwamnati.
Nana Addo dai ya dade yana
neman takarar shugabancin Kasar tun a shekarar 1998. Sai dai wannan karo ya
samu. Haka a Najeriya Shugaba Buhari ya gwabza sau da dama kafin Allah yayi. Duk sun sha bugewa a Kotu
Muhammad Malumfashi
NAIJ Hausa
No comments:
Post a Comment