– Kungiyar ECOWAS na shirin tunbuke Shugaban Kasar Gambia Yahaya Jammeh
– ECOWAS tace ta tanadi Sojojin da
za su kutsa Gambia domin ganin bayan Jammeh ko babu
girma, ba arziki
– Shugaban Kasar ya fadi zabe, ya kuma ce ba zai sauka
ba
Rikicin siyasar Kasar Gambia
na ta kara cabewa bayan da Kungiyar ECOWAS ya Kasashen Afrika ta Yamma ta ce za
ta cire Shugaban Kasar Gambia ko ya ki-ko ya so. ECOWAS tace ta shirya Rundunar
Soji da suka shirya tunbuke Yahaya Jammeh.
Yanzu haka dai Shugaba
Buhari ya taka har Kasar, inda ya zarce zuwa Mali domin ganin Shugaban Kasar na
Gambia ya sauka daga mulki bayan ya sha kayi a zabe. Kasashen sashin Nahiyar
dai suna shirin hada Runduna domin tinkarar Kasar Gambia da Shugaban Kasa
Jammeh.
Jaridar Punch ta bayyana
cewa Kasashen na Afrika na neman izini daga Majalisar dinkin Duniya domin far
wa Kasar ta Gambia, ba girma ba arziki. Wani Manzo na Majalisar Dinkin Duniyar,
Muhammad Ibn Chambas yace ko ta halin kaka sai an sauke Jammeh an daura Adama
Barrowa wanda ya lashe zabe.
Kwanakin baya ne Shugaban Kasar
Gambia ya sanar a Gidan Talabiji cewa ba abin da zai sa ya sauka daga
Shugabancin Kasar bayan shekaru fiye da 20 yana kai. Ya dai sha kashi a zaben takarar da aka yi a bara.
[A duba shafin NAIJ Hausa domin samun labarai da dumi-dumi]
No comments:
Post a Comment