– An fara fafatukan neman Jihar Kudancin Kaduna
– Yankin
dai na ta fama da rikici dabam-dabam
– Wani
Fasto ya nemi Shugaban Kasa ya zamar da Yankin Jiha mai zaman kan-ta
Masu kira sun fara kira da a
ba Yankin Kudancin Kaduna Jiha mai cin gashin-kan ta. Sakataren Kungiyar
Fentakwastal ta Kiristocin Najeriya Emmanuel Nuhu Kure ya fara wannan kira.
Rikivin Yankin ya sa Faston yayi wannan kira.
Sakataren na Kungiyar PFN
yace ya dace Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya mayar da Yankin Kudancin Kaduna
ta zama Jiha mai zaman kan ta. Kure yace idan har aka yi hakan, za a yi maganin
rikicin da ake tayi tsakanin Fulani Makiyaya da mazauna Yankin.
Fasto Emmanuel ya bayyana
haka ne ga manema labarai a wata magana da aka yi da shi a wayar tarho. Fasto
Emmanuel Nuhu Kure yace idan neman zaman lafiya kurum a ba Mutanen Yankin Jiha
guda, yace ko dama can duk Kiristoci ne.
Kwanan nan Shugaba Muhammadu
Buhari ya gana da Shugabannin Hafsun Sojojin Kasar nan wajen ganin kawo karshen
rikicin Kudancin Jihar Kaduna da sauran
Yankuna da ake tada rikici irin su Neja-Delta. Faston ya yabawa Shugaban Kasar
da wannan kokari.
No comments:
Post a Comment