– NNPC tayi magana game da rade-radin karin farashin man fetur
–
Kamfanin NNPC tace ba za ta kara farashin man fetur ba
– Kwanaki
Gwamnatin Shugaba Buhari ta cire tallafin man fetur
Kamfanin NNPC na mai na Kasa
ta yi magana game da rade-radin da ake tayi na cewa za a kara kudin fetur a
Kasar. NNPC tace babu maganar karin farashin man na fetur kamar yadda Jama’a ke
fada.
Haka kuma NNPC sun yi kira
da Jama’a su kwantar da hankalin su domin kuwa akwai mai a kasa. Jama’a dai na
ta sayen dinbin mai suna ajiyewa gudun matsala nan gaba. NNPC dai tace tana da
sama da lita biliyan daya na mai ajiye.
NNPC dai sun ce man da take
da shi a ajiye zai isa Najeriya har na fiye da wata guda. Matatar man Najeriya
duk sun fara aiki don haka babu maganar a samu karancin kanaziri ko man babbar
mota. Wani Babban Jami’in NNPC, Mista Anibor Kragha ya bayyana haka da yake magana
a Majalisar Wakilai ta Tarayya.
Mataimakin Shugaban Kasa,
Farfesa Yemi Osinbajo yace nan da ‘Yan shekaru mai zai zama ba komai ba a
Duniya. Osinbajo ya kai ziyara Neja-Delta inda Gwamnati ke kokarin kawo karshen
rikicin Yankin.
.
[NAIJ Hausa]
No comments:
Post a Comment