– Masu
jigilar mai sun tabbatar da cewa babu maganar kara farashin man fetur
–
‘Yan kasuwan sun ce babu wannan shiri a yanzu
– Kwanaki aka fara jitar-jitar watakila farashin fetur
zai tashi
Kungiyar masu jigilar main a
Kasar nan ta bayyana cewa babu maganar karin farashin kudin man fetur. Kungiyar
ta IPMAN na bangaren Kano tace Jama’a su daina daukar maganar cewa kudin mai
zai daga.
Alhaji Bashir Dan Malam
wanda shine Shugaban Kungiyar ta IPMAN a Kano yace za a kama duk wadanda suka
sayar da mai a sama da farashin da Gwamnati ta saka. A Kano dai cikin ‘yan
kwanakin nan mun samu labarin ana sayar da litan man fetur har a kan N155.
Dan Malam ya fadawa Hukumar
Dillacin labarai cewa babu wani shiri na kara farashin man fetur din. Shugaban
Kungiyar yace jita-jita ne kurum maras tushe. Dan Malam yace sun zauna da
Gwamnati sun kuma shawo kan sabanin da suka samu na kudin don haka farashin mai
na nan yadda aka sani.
Kwanaki NNPC dai suka ce man
da su ke da shi a ajiye zai isa Najeriya har na fiye da wata guda. Matatar man
Najeriya duk sun fara aiki don haka babu maganar a samu karancin kanaziri ko man
babbar mota.
[NAIJ Hausa]
No comments:
Post a Comment