Sunday, January 29, 2017

Ba mu da shirin kara kudin man fetur-Inji ‘Yan kasuwa


Masu jigilar mai sun tabbatar da cewa babu maganar kara farashin man fetur


‘Yan kasuwan sun ce babu wannan shiri a yanzu


Kwanaki aka fara jitar-jitar watakila farashin fetur zai tashi





Kungiyar masu jigilar main a Kasar nan ta bayyana cewa babu maganar karin farashin kudin man fetur. Kungiyar ta IPMAN na bangaren Kano tace Jama’a su daina daukar maganar cewa kudin mai zai daga.

Alhaji Bashir Dan Malam wanda shine Shugaban Kungiyar ta IPMAN a Kano yace za a kama duk wadanda suka sayar da mai a sama da farashin da Gwamnati ta saka. A Kano dai cikin ‘yan kwanakin nan mun samu labarin ana sayar da litan man fetur har a kan N155.

Dan Malam ya fadawa Hukumar Dillacin labarai cewa babu wani shiri na kara farashin man fetur din. Shugaban Kungiyar yace jita-jita ne kurum maras tushe. Dan Malam yace sun zauna da Gwamnati sun kuma shawo kan sabanin da suka samu na kudin don haka farashin mai na nan yadda aka sani.

Kwanaki NNPC dai suka ce man da su ke da shi a ajiye zai isa Najeriya har na fiye da wata guda. Matatar man Najeriya duk sun fara aiki don haka babu maganar a samu karancin kanaziri ko man babbar mota.


[NAIJ Hausa]

No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...