– ‘Yan
Majalisun Kasar nan na shirin fara zama domin kasafin kudin wannan shekarar
– Majalisar
Dattawa za ta fara zama game da kundin kasafin kudi
– Watakila yau Majalisar Dattawar ta tabbatar da Magu
Rahotanni daga Jaridar Daily
Trust na nuna cewa yau Majalisar Dattawa za ta fara zama domin ta tattauna abin
da ya shafi kundin kasafin wannan shekarar. Sanata Baba Garbai Kaka wanda shine Shugaban Kwamitin irin wannan
al’amura ya bayyana haka.
Shugaban kasa Muhammadu
Buhari ya gabatar da kasafin kudin a gaban Majalisar a karshen shekarar bara.
Sai dai Majalisar ba ta ce komai ba tukun game da kundin har yanzu. Majalisar
dai kwanaki tace tana da ayyuka da dama a gaban ta kamar su maganar rikicin
Kudancin Kaduna da kuma haramta shigo da motoci, ga kuma kudirin PIB na
bangaren mai.
Idan ba a manta ba kwanakin
bayan ne Majalisar ta karkare batun takardun MTEF da kuma FSP da Shugaban Kasa
ya kawo a baya. Zuwa wannan makon dai Sanatocin Kasar za su shiga tattauna game
da kasafin bana wanda ya zarce Naira Tiriliyan 7.
Har wa yau kuma ana sa ran
yau Shugaban Majalisar, Bukola Saraki ya kara karanto takardar shugaban kasa da
ya ke nema a tabattar da Ibrahim Magu a matsayin Shugaban Hukumar EFCC. A
kwanakin baya dai Majalisa ta kora Ibrahim Magu bisa wasu dalilai.
No comments:
Post a Comment