Wani Malami ya dubo lokacin da
Shugaba Buhari zai mutu
– Wani Malamin Addinin Kirista yace Shugaba Buhari ya kusa mutuwa
– Sannan Faston yace Kasar
Biyafara za ta balle
– Wannan dai yana cikin duban da ya
gano
Wani
Fasto a Najeriya ya buga-ya gano cewa Shugaba Buhari ba zai karasa mulkin Kasar
nan ba. Malamin Addinin Kiristan ya bayyana cewa ya leko cewa Shugaba Buhari
zai rasu ne a cikin shekarar 2019 inda rashin lafiya za ta ci sa.
Faston
yace Farfesa Osinbajo, Mataimakin Shugaban Kasar ne zai karbi mulki, kuma zai
fuskanci kalubale wajen jagorantar Kasar daga hannun Soji. Wannan dai harsashen
wani Fasto ne mai suna Emmanuel Chukwudi da ke Garin Asaba.
Babban
Faston da ke Jihar Delta ya bayyana irin abubuwan da ya hango cewa za su wakana
a shekarar nan. Yake karawa da cewa za a saki Nnamdi Kanu daga Kotu, kuma har a
cin ma samun Kasar Biyafara.
Malamin
yace an nuna masa cewa dai Najeriya za ta fita daga matsalar tattalin arziki a
bana. Mafi yawan Fastoci dai su kan yi nasu harsashen daga abin da suka gano.
Sai dai mafi yawancin duk tamkar kanzon-kurege ne, don akasarin hakan ba su
faruwa. A Jiya ne ma dai wani Faston yace Shugaba Buhari zai yi shekaru 8 a mulki.
[NAIJ Hausa]
No comments:
Post a Comment