Sunday, January 15, 2017

Gwamnati ta kira ‘Yan BBOG zuwa ceto ‘Yan Chibok


BBOG ku zo mu shiga Sambisa da ku-Gwamnatin Najeriya


Gwamnatin Najeriya sun gayyaci ‘Yan Kungiyar BBOG zuwa ceto ‘Yan matan nan na Chibok


Ministan yada labarai, Alhaji Lai Muhammad ya gayyaci ‘Ya Kungiyar a wata wasika


Ministan ya nemi ‘Yan Kungiyar su aika Mutane 3 domin a shiga Dajin Sambisa da su




Gwamnatin tarayya ta Najeriya ta Ministan yada labarai, Alhaji Lai Muhammad ya gayyaci ‘Ya Kungiyar nan ta BBOG watau BringBackOurGirls zuwa ceto ragowar ‘Yan matan nan da aka sace shekarun baya a Garin Chibok.

Ministan ya nemi ‘Yan Kungiyar su tura Mutane 3 domin a shiga Dajin Sambisa da su domin su ganewa idanun su irin aikin da Sojin Kasar ke yi. Ministan ya aika wannan wasika ne inda yake jinjinwa ‘Yan Kungiyar da kokarin na ganin an ceto ‘Yan matan na Chibok.

Cikin wadanda za su shiga wannan aiki akwai Shugaban Hafsun Sojojin sama na Kasar da kan sa da shi Ministan da kuma Ministan tsaro na Kasar. Sai dai anya kuwa ‘Yan Kungiyar za su amsa wannan goron gayyata na ceto ‘Yan matan da suka yi kwana 1000 suna tattaki a kan su?

'Yan Kungiyar na BBOG dai sun bada wasu sharudda kafin su amince da wannan tayi. Madam Oby Ezekwensili ta bayyana cewa har sai an nemi afuwan su a kan wani kaifi da aka yi masu a baya kafin su karbi wannan tayi.


[Daga NAIJ Hausa]







No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...