Don nace ayi gaskiya suka tunbuke
ni-Ndume
– Sanata Ali Ndume ya bayyana dalilin da ya sa aka tunbuke sa daga kujerar sa
– Majalisar Dattawa na Kasar ta
cire Sanata Ali Ndume daga matsayin sa jiya
– Ashe a dalilin Magu ne aka cire Ndume
Sanata
Ali Ndume ya bayyana zunubin da ya aikata da har ta sa aka cire sa daga
Shugaban masu rinjaye a Majalisar Dattawar Kasar. A jiya ne dai Shugaban
Majalisa, Bukola Saraki ya karanta wata takarda daga ‘Yan APC mai nuna cewa sun
cire Sanata Ndume daga matsayin sa.
Ali
Ndume yayi wata hira da Jaridar Premium Times inda ya bayyana dalilin da ya sa
aka cire sa. Ndume yace don ya nemi Majalisa ta yi gaskiya wajen tantance
Ibrahim Magu na EFCC shiyasa aka sauke sa. Tun daga nan ‘ya ‘yan Jam’iyya suka
fara kokarin juya masa baya.
Ndume
yace ba a bi matakan da suka dace wajen kin tabbatar da Magu ba a matsayin
Shugaban EFCC. Sanatan yace ba a bada dama domin ya wanke kan sa ba, sai dai
kurum aka bayyana cewa Majalisar ba ta aminta da shi ba. Ndume yace kus-kus
kawai aka yi wajen tabbatar da Magu, daukacin Majalisa ba ta zauna ba.
Dama
can ana ta samun wasu bayanai masu cin-karo da juna a Majalisar. Sanata David
Ummaru yace sam ba a tattauna maganar tantance Magu ba ko rashin hakan a zaman
Majalisar. Sanata Ummaru dai shi ne Shugaban Kwamitin shari’a na Majalisar
Dattawar Kasar.
Kafin dai Ahmed Lawan ya je yayi Sallah ya dawo, sai dai ya ji labarin har an tsige sa daga matsayin. Yanzu haka muna samun labarin cewa Jam'iyyar APC tayi na'am da wannan abu. Tuni dai an nada Ahmed Lawan a matsayin wanda zai maye gurbin na sa. Sanata Marafa yace saura kuma kujerar Ikweremadu
No comments:
Post a Comment