Thursday, January 26, 2017

An shiga uku: Trump ya fara fatattako 'Yan Afrika


– Sabon Shugaban Kasar Amurka ya fara koro bakaken Afrika da suka tare Amurka gida


Trump ya sa kafar wando daya da bakin haure


Donald Trump kuma ya fara shirin gina katangar karfe tsakanin sa da makwabta





Sabon shugaban Kasar Amruka, Donald Trump ya sha alwashin kare kaimi wajen bakin iyakokin Kasar Amurka saboda masu shigowa su tare a Kasar ba a san da su ba. Yanzu haka dai har Trump ya fatattako ‘Yan Afrika kusa 100 gida.

A Ranar Laraba ta Jiya sabon shugaban Kasar ya fatattako bakin haure a Kasar har guda 92. A Ranar ne kuma Shugaba Trump din ya fara shirin gina katangar karfe tsakanin Kasar Amurka da makwabta Kasar Mexico.

Cikin wanda Trump ya koro akwai mutanen Kasar Somalia, da kuma Kenya, wadanda aka tusa keyarsu har filin jirgi. Har wa yau dai sabon Shugaban ya hana a bada takardar shiga Kasar Amurka ga mutanen Kasar Yemen, Iraki, Iran, Somaliya, Sudan, da kuma Kasar Siriya.

Har wa yau kuma Kasar Amurka na shirin aika Dalibai zuwa Duniyar wata domin su girka giya kamar dai yadda muka samu labarai daga Birnin Los Angeles na Kasar Amurka. Wannan ne dai karo na farko a tarihi da Amurka tayi irin wannan abu.


[NAIJ Hausa]

No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...