Wednesday, January 11, 2017

An gano masu tada rikicin Kudancin Kaduna-Gwamna El-Rufa'i


Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufa’i ya bayyana cewa ya kama masu tada rikicin Kaduna


Gwamnan ya bayyaa sunayen wadanda aka kama da laifi


Mal El-Rufa’i ya kai ziyara Ofishin Kwamishinan ‘Yan Sanda na Jihar




Gwamnatin Jihar Kaduna ta bayyana cewa ta gano, ta kuma kama wadanda ke da laifi a cikin rikicin Kudancin Jihar Kaduna. Gwamna Nasir Ahmed El-Rufa’i ya bayyana haka yayin da ya kai ziyara Ofishin Kwamishinan ‘Yan Sanda.

Malam Nasir El-Rufa’i ya bayyana sunayen wadanda aka kama lokacin da ya kai ziyara Ofishin Agyle Abeh, Kwamishinan ‘Yan Sanda na Jihar Kaduna. Duk da yake Gwamnan bai bayyana sunayen masu tada rikicin a fili ba, yayi alkawarin hukunta masu laifin.

Gwamnan Jihar yace ba za su kyale a rika abin da aka ga dama ba a Jihar na rikici tsakanin Fulani Makiyaya da kuma ‘Yan Gari wanda an dade ana fama. Har dai wasu na ganin abin kamar rikicin addini



[NAIJ Hausa]

No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...