Monday, January 2, 2017

A komawa Allah-Inji Obasanjo

Obasanjo yace ‘Yan Najeriya su komawa Allah




– Tsohon Shugaban Kasar Najeriya ya ce dole ‘Yan Najeriya su komawa Ubangiji


Cif Obasanjo yayi wannan kira ne a Garin Ogun


Ana ta murnar shiga sabuwar shekarar Miladiyya


Tsohon Shugaban Kasa Cif Olusegun Obasanjo yace dole ‘Yan Kasa su komawa Ubangiji idan har suna so abubuwa suyi kyau a shekarar nan da aka shiga. Tsohon Shugaban Kasar yayi wannan kira ne a Garin su.

Jaridar Vanguard ta rahoto cewa Tsohon Shugaban Kasan yayi wannan kira ga ‘Yan Najeriyar ne bayan an gama Ibada a wani Coci da ke Garin Abeokuta na Jihar Ogun domin murnar shiga sabuwar shekarar 2017.

Cif Olusegun Obasanjo dai ya bayyana cewa a komai za a yi sai an saka Allah; siyasa ne ko harkar tattalin arziki ne ko ma zamantakewa na rayuwa ne dole a tuna Ubangiji. Tsohon Shugaban Kasar dai yace yana sa rai abubuwa za su yi kyau.

Kwanakin baya ne Shugaban Jam’iyyar APC mai mulki, Cif John Odigie-Oyegun yace Ubangiji ne ya aikowa Kasar Najeriya Shugaba Buhari domin gyara ta. Shugaban Jam’iyyar APC yayi wannan jawabi ne a wani lokaci a Garin Sokoto wajen taron ‘Ya ‘yan Jam’iyyar na Jihar Kano.



[NAIJ Hausa] 


No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...