Monday, January 30, 2017

An takawa Donald Trump burki


– Sabon Shugaban Kasar Amurka ya bada umarnin hana wasu baki shigowa Kasar Amurka


– Sai dai kuma Kotu ta dakatar da wannan shiri na Shugaban Kasar


Wasu Kasashen sun fara maida martani




Kwanan nan, sabon shugaban Kasar Amurka, Donald Trump ya saka hannu kan wata doka da ta hana baki shiga cikin Kasar Amurkar. Hakan dai ya sa aka tsare mutane kusan 200 da suke kokarin shigowa a filin jirgi.

Wata Kotu da ke Brooklyn ce dai ta cece Jama’a, inda wani Alkali ya hana dabbaga wannan doka ta sabon shugaban Kasa Donald Trump. Wannan doka dai ta Donald Trump ta shafi har wadanda suke dauke da katin zama ‘Yan Kasar Amurka. 


Ana ta zanga-zanga a Amurka, wasu ma na shirin neman rabewa daga Kasar


A Ranar Juma’a Donald Trump dai ya nemi a hana bakin da ‘yan gudun hijira shigowa cikin Kasar na watanni hudu yayin da ya kuma haramtawa ‘Yan Kasar Siriya shigowa Amurkar har abada. Kasar Iran dai wannan abu bai yi mata dadi ba, kuma ta fara shirin hana Amurkawa shigan Kasar.

A wani harsashe da NAIJ.com tayi, an fahimci cewa ‘Yan Najeriya masu takardar shaidar zama ‘yan wata Kasar na iya fuskantar kalubale musamman idan dayar Kasar ta su tana cikin guda 7 da Trump ya hana shiga Amurka.


[NAIJ Hausa]

No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...