Saturday, January 21, 2017

Hudubar Jumu’a daga Masallacin I.T.N



Hudubar Jumu’a daga Masallacin I.T.N Zangon-Shanu, Zaria



RAUNIN MUSULMAI A YAU


Daga Bakin Malam Farfesa Ibrahim Ahmed Aliyu


A’udh BilLahi minas-Shaidanir Rajim…BismilalLahi Rahmanir Rahim
Dukkan yabo sun tabbata ga Allah wanda ya shiryar da mu zuwa addinin Musulunci. Muna shaidawa babu abin bauta da gaskiya sai Allah; wanda ya bamu addinin da ya fi kowane addini watau Musulunci. Muna tabbatawa Annabi Muhammadu SAW bawa ne kuma Manzo wanda ya cika alkawari. Duk wanda ya bi addinin Musulunci, tabbas ya samu gyadar dogo. Allah ya dada tsira ga Annabin Sa, ya sa mu kuma mu tabbata cikin Musulunci.
Bayan haka:
‘Yanuwa Musulmai, da can a baya, Mu ne a gaban ayari, Mu ne ke rike da linzami na ragamar al’ummar Duniya na wani lokaci. Mun yi jagoranci cigaban da babu irin sa a da. A wancan lokacin, Musulmai sun hada ilmin Duniya da na lahira watau hasken wahayi da na hankali. Cigaban Musulunci ya zama cigaba da babu irin sa, harshen musulunci shi ne ya zama harshen cigaba. Jami’o’in Musulunci su ne wuri na karatu ga dukkanin mutane daga ko ina a Duniya. Litattafan Muslunci sune madogara a Duniya. Sunayen Malaman Musulunci ke haskaka ko ina a Duniya. Kai karfin Musulmi ya kai lokacin da Khalifa Umaru Dan AbdulAziz ya ji labarin cewa an kama wani Musulmi a matsayin Fursunan Yaki, Khalifa Umar AbdulAziz ya rubutawa Sarkin Rumawa takarda cewa: ‘Bayan gaisuwa, naji labarin ka kama wani Musulmi, wanda Allah ya rubutawa martaba, sai kai ka wulakanta sa. Ina maka kashedi cewa idan har wasika ta, ta zo maka, to ka sake sa. Idan ba haka ba, zan zo maka da runduna wanda karshen ta inda kake, farkon ta kuma inda nake…’ Girma da daukakan Musulmi ya kai wani Khalifa na Daular Abassiya ya taba fadawa wani girgije na damina a sararin samaniya: ‘Ya kai girgije, ko kayi gabas, ko kayi yamma, ka yi ruwa inda duk ka ga dama, harajin ka sai ya zo ga Baitul-Mali na Musulmai…’ Ma’ana ko yayi ruwa Kasar Musulmai, a samu Zakkah, ko kuwa inda ba su ba, a samu haraji na jizya daga hannun wadanda ba Musulmai ba. A da can Musulmai ke rike da Duniya, lokacin da muke rike da Musulunci. A lokacin akwai jin dadi da kwanciyar hankali, sai dai lokacin da aka rabu da Musulunci sai muka zama kaskantattu.
Ya ‘yan uwa yanzu muna nan a danne mu, ana tursasa mu, mun zama koma-baya, ana yi mana cin kashi. Ko me ya jawo haka? Shin ba mu da yawa ne? A’a! Wallahi muna da yawa! Yawan Musulmai yanzu ya kusa Biliyan 2, sai dai yawan namu bai da amfani tamkar yawan tsintsiya ba shara; kamar dai yadda Manzo SAW ya fada za mu zama kamar sharan bisa ruwa, a wannan lokaci Al’ummomi za su rika wasoso a kan mu, kamar yadda mayunwata suke wasoso a kan akushi. Dama Manzon Allah SAW yace za a cire kwarjinin Musulmai a fuskar Mutane, sannan kuma za a same mu da rauni. Ko menene wannan rauni da Manzon Allah SAW ya fada? Wannan rauni shine son duniya da tsoron mutuwa. Sai ka ga mai rauni a da baya yayi galaba a kan musulmi. Masu tsoron mutuwa sun afka mana, har kaskantattu sun koma suna mana cin kashi. To gaskiya lalacewar zukatan mu ne ya jawo duk wadannan abubuwa suka faru, ba shakka mun yi rauni kamar yadda Annabi SAW ya fada.
‘Yan uwa Musulmi a gaskiya mun bar Musulunci, Allah SWT kuma ya bar mu. Ubangiji ya bar mu da kawun mu, kuma duk wanda Allah SWT ya bari da kan sa, ba zai taba samun nasara ba a nan Duniya da Lahira. Mafita kuma itace a komawa Musulunci, dole mu komawa Addinin Musulunci gaba dayan mu. Musulunci kuma ba shi bane kafa dokoki watau haddi na zina ko bulalan shan giya. Bari ma wannan wani bangare ne kadan daga cikin bangarorin Musulunci; Surorin da suka saukar da Hukuncin laifuffuka sune karshe daga cikin abin da aka saukar a Al-kur’ani. Ayoyin da suka yi magana game da laifuffuka kididdigaggu ne idan aka kamanta da sauron Ayoyi, ba dai wadannan bane kadai Addinin Musulunci. Saboda haka dole ne mu koma yi wa Jama’a kyakkyawar tarbiya, tarbiya da za ta hana mutane bata daga hanyar Allah. Mutane da dama dai sun fi damuwa da kafa dokokin Musulunci, wanda ko ba ya gina al’umma ko raya zukata. Abin da ke gina Mutane shi ne tarbiya. Tun daga Gidajen mu da kuma Makarantu da hanyoyin sadarwa za a yi wannan aiki na tarbiya. Da irin wannan tarbiya ne mutum zai zama Musulmi na gari a ko yaushe yana tsoron Allah ba tare da wani Dan Sanda ba. Mutum ya zama kamar wannan Budurwar nan ta zamanin Sayyidina Umaru RA da ta ki kara ruwa cikin nono yayin da uwar ta ke nema tayi algush, Budurwa tace da Uwa ta: Ai Umar RA  ya hana, sai Uwar tace: ‘Ai Umar RA bay a ganin mu..’ Budurwa kuwa tace: ‘ai Ubangijin Umaru yana ganin mu... Ko kamar Makiyayin nan da yace da Umaru RA ‘Ina Allah SWT yake?’ yayin da ya nemi jarraba Bawan nan da ya cuci Ubangidan sa. Saboda haka Umaru RA ya ‘yan ta wannan Bawa yace idan ya ci gaba a haka, za a ‘yan ta sa a Gobe Kiyama.
Ya ‘yan uwa lokaci yayi da za mu gane mu su waye. Mu fa Musulmai ne, kuma dole mu rike Musulunci. Idan har mu ka rike Musulunci; muna tare da komai, idan kuma mu ka bar Musulunci; ba mu da komai. Babu kuma wanda ya isa ya hana mu wannan Addini. Abin da muke so shine mu rayu, kuma mu mutu a Musulunci, muna masu takama da wannan Addini. Allah SWT dai yace babu wanda ya fi kyakkyawar magana kamar wanda yayi aiki na kwarai yayi kira ga Allah, ya kuma ce ina cikin Musulmai.
Allah ka daukaka mu, ka wulakantar da abokan gaban mu. Allah muna hada ka da abokan gaban mu. Allah ka sa mana kin kafirci da fasikanci da sabon ka. Allah ka sanya mu cikin rahamar ka.
Ameen.


Muhammad Malumfashi yayi aikin wannan huduba daga Zaria.
Twitter: @Ya_waliyyi



No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...