– Masana
sun yi gargadi game da cin kifin nan mai suna kurungu
– Cin kifin yana jawo cuta a jikin Dan Adam
– Kwararru
sun kira ‘Yan Najeriya su rage amfani da kurungu a miya
Ashe Kurungu da nada illa?
Kwararru sun yi gargadi game
da cin kifin nan da aka sani da suna kurungu, suka ce yawan cin san a kawo cuta
a jikin Dan Adam. Wani Likita mai suna Dakta Arikawe Adeolu yake bayyana haka a
Garin Abuja.
Babban Likitan da ke aiki a
Asibitin Tarayya na Jabi da ke Abuja yake bayyanawa wajen wata hira da aka yi
da shi cewa kifin nan kurungu yana da illa a jikin Mutum. Daktan yace kifin na
dauke da wasu sinadarai da aka iya jawo kumburi a jika.
Dakta Adeolu yace kifin na
iya jawo cutar hawan jini da ciwon sukari idan ba a bi a hankali ba. A Najeriya
dai an saba shan farfesun irin wannan kifi. Akwai abin da ake kira fatty acid, wannan sinadari yana da
tasari ga abin da ake kira kwalastaral.
A can Jihar Ekiti kuwa Yanzu
haka har farfesun kare ake yi a wasu wuraren. Abin dai har ta kai babu karnuka
a kan titi, don kuwa tuni sun shige tukunya.
Yanzu haka Karnuka sun fara
bacewa a Jihar Ekiti, domin kuwa duk inda ka shiga cin abinci sai dai ka ga
naman kare a cikin miya. Mutanen Jihar Ekiti dai sun komawa naman karnuka.
Hukumar Dillacin labarai na Kasa ta bada wannan labara. Haka zalika, Sai dai
masana sun ce naman kare yana da illa kwarai a jikin Dan Adam.
No comments:
Post a Comment