– Hukumar Kwastam na neman wasu
Ma’aikatan ta ruwa-a-jallo
– Wadannan Jami’ai biyu suna
da hannu wajen shigo da wasu tarin makamai
– Duk wanda ya ga wadannan Jami’ai
ana bukatar ya nemi Hukuma
Hukumar
Kwastam ta sanar da cewa tana neman wasu Ma’aikatan ta guda biyu ruwa-ajallo.
Wadannan Ma’aikata suna da hannu wajen shigo da wasu tarin makamai cikin Kasar
ta hanyar Legas.
Idan
ba a manta ba Ranar Lahadi ne Hamid Ali wanda shine Shugaban Hukumar ta Kwastam
din ya bayyana cewa an samu datse wasu kwalaye dauki da tulin bindigogi. An dai
samu sababbin bindigogi har guda 661 fil a cikin kwali ana neman a shigo da su
cikin Kasar.
Yanzu
haka dai Hukumar Kwastam na neman Ma’aikatan na ta biyu da ke da hannu wajen
shigowa da wadannan makamai; Abdullahi I da kuma Odiba Haruna Inah. Ana neman
duk wanda ya gan su ya hanzarta ya sanar da Hukumar Kwastam.
Tuni
dama dai aka kama mutane 3 da ke da hannu wajen shigo da makaman daga ciki
akwai wanda ya shigo da su cikin Kasar Oscan Okafor da kuma wasu; Mahmud Hassan
da Sadique Mustafa.
[NAIJ Hausa]
No comments:
Post a Comment