Tuesday, January 17, 2017

Daga cewa Shugaban Kasa zai mutu.. An kama sa

‘Yan Sanda sun kama wani don yace Shugaba Mugabe zai mutu




– Jami’an ‘Yan Sanda sun damke wani Fasto bayan ya bayyana ranar da shugaban kasa zai rasu


– Faston yace Mugabe zai rasu a watan Oktoban shekarar nan


– A Kasar Zimbabwe dai bai halatta kace shugaban kasa zai mutu ba


An ce a bakin wawa ake jin mutuwar sarki. Ga wani Fasto ya gano ranar da shugaban kasa zai mutu. Ko da ya bayyana kuwa, sai ‘Yan Sanda kuma kama sa da laifi. Yanzu haka Patrick Mugadaza na hannun Jami’ai.

Wani Faston Cocin Kariba mai suna Patrick Mugadaza ya bayyana cewa shugaban kasar Zimbabwe, Robert Mugabe zai rasu a cikin watan Oktoban wannan shekarar, ko da ya sanar da hakan sai ‘Yan Sanda suka kama shi. Shugaba Mugabe dai yana da shekara 93 a Duniya ya kuma dade kwarai kan mulki.

A wancan makon ne Faston yace an nuna masa cewa Mugabe zai rasu a Ranar 17 ga watan Oktoban bana. A Kasar ta Zimbabwe bai halatta kace shugaban kasa zai mutu ba. Don haka tuni ya shiga hannun Hukuma.

A nan gida kuwa, kwanakin baya wani Fasto a Najeriya ya buga-ya gano cewa Shugaba Buhari ba zai karasa mulkin Kasar nan ba. Malamin Addinin Kiristan ya bayyana cewa ya leko cewa Shugaba Buhari zai rasu ne a cikin shekarar 2019 inda rashin lafiya za ta ci sa.





[NAIJ Hausa]

No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...