– Wani
Malamin Asibiti ya fada hannun miyagu masu garkuwa da mutane a Sokoto
– Kungiyar Malaman Asibiti na Jihar Sokoto ta bayyana
haka
– Satar Jama’a dai ya zama ruwan dare a Kasar nan
Jaridar Premium Times ta
rahoto cewa an sace wani Malamin Asibiti a Garin Sokoto. Shugaban Kungiyar
Malaman asibiti na Jihar, Abdullahi Aliyu ya bada wannan sanarwa ba da dadewa
ba. Sunan wannan Jami’in Asibiti dai Bello Arzika.
Abdullahi Aliyu yace an sace
daya daga cikin ‘ya ‘yan Kungiyar na sun a Malaman asibitin Najeriya watau
MHUN. An sace Malamin lafiyar ne a Yau Litini kamar yadda Aliyu ya bayyanawa
manema labarai. An dai yi gaba da Malamin ne bayan ‘Yan fashi sun tare su.
An sace Bello Arzika ne a
hanyar Sokoto zuwa Isa kamar yadda NAN mai dillacin labarai ta bayyana. Yanzu
dai an shiga Dajin Gundumi da Malamin kiwon lafiyar. Jami’an tsaro dai sun ce
ba su da masaniya game da lamarin.
Arzika ya taba rike wani matsayi a Kungiyar ta Malaman asibitin Najeriya watau MHUN na shiyar Sokoto.
Sata da garkuwa da Jama’a
dai ya zama ruwan dare a Kasar, haka kwanaki a ka kama wani Tsohon Malamin
Jami’ar Ahmadu Bello ta Zariya a hanyar sa ta Abuja.
[NAIJ Hausa]
No comments:
Post a Comment