Thursday, January 5, 2017

LABARI DA DUMI-DUMI: An ceto wata ‘Yar Chibok


Sojojin Najeriya sun kara ceto wata daga cikin ‘Yan Matan nan da aka sace a Chibok


Jaridar Sahara Reporters tace an tsinci yarinyar da goyo


Kusan kwanaki 1000 kenan da sace ‘Yan Matan daga Makarantar su




A yayin da ake bakin cikin cikar kwanaki 1000 da Boko Haram suka sace Yan Matan nan na Chibok daga Makarantar su, Sojojin Najeriya sun ga guda 1 daga cikin su a wajen Dajen Sambisa.

Labarai daga Sahara Reporters na nuna cewa an samu Yarinyar ne tare da goyon wani da ake tunani na ta ne. Sunan wannan Yarinya dai da Sojojin Bataliya ta 27 suka kubutar Rakiya Abubakar.


An sami wannan Yarinya ne a Ajigin da ke Karamar Hukumar Damboa. Wannan dai itace kusan ta 29 da ta baro hannun Boko Haram tun bayana da aka sace su shekaru fiye da biyu da suka wuce. An dai sace ‘Yan mata fiye da 200 a wancan lokaci.

Kwanaki dai an ceci wasu daga cikin ‘Yan matan har wani Gwamna yake cewa kawai ana kokarin kauda hankalin ‘Yan Najeriya ne daga halin da ake ciki a fadin Kasar na yunwa da talauci.


[NAIJ Hausa]



No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...