– Wani Tsohon Dan Majalisa ya mace
a hannun Jami’an ‘Yan Sanda a Legas
– An dai tsare Honarabul Nze Duru
ne a Ranar Alhamis, ya kuma cika Ranar Juma’a
– Sufeta Janar na ‘Yan Sanda ne dai
ya sa aka kama sa
Wani
Tsohon Dan Majalisar Kasar nan Honarabul Nze Duru ya cika a hannun ‘Yan Sanda a
Ranar Jumua’ar da ta wuce. Jami’an ‘Yan Sanda sun kama Nze Duru a Legas a Ranar
Alhamis, ya kuma ce ga Garin ku nan a Ranar Jumu’a.
Rahotanni
na nuna cewa Sufeta na ‘Yan Sanda; Ibrahim K Idris ne ya bada umarnin kamo
Tsohon Dan Majalisar. Honarabul Nze dai ya rasu ne a cikin dakin da yake tsare
da ke Onikan a Jihar Legas. Ana zargin Honarabul din da yin gaba da wasu kudin
fansho, sai dai a lokacin ya karyata zargin ya kuma zargi Jami’an ‘Yan Sanda da
nuna rashin gaskiya a lamarin binciken.
A
Gidan tsarin ne dai Honarabul din ya yanke jiki ya fadi. Honarabul Nze Duru ya
bayyana cewa Mataimakin Sufeta Janar na ‘Yan Sanda na Yankin Legas, Aderanti
Kayode ya hana sa ganin Likita har sai da abubuwa suka tabarbare.
[NAIJ Hausa]
No comments:
Post a Comment