Wednesday, January 18, 2017

An samu subul-da-bam a Yankin IDP


– A jiya ne aka samu wani kuskure daga Sojin Najeriya


– Rundunar Sojin saman Kasar sun saki wani bam a sansanin ‘Yan gudun Hijira ba da sani ba


Mutane kusan 2 ne kuma suka rasa rayukan su



A jiya ne dai aka samu wani matsala daga Sojojin Najeriya; Sojin saman Kasar sun yi wani subul-da-bam a sansanin ‘Yan gudun Hijira da ke Garin Rann. Wannan yayi sanadiyar mutuwar mutane 2, da dama kuma sun raunana.

Shugaban Kasa yayi maza-maza ya mika ta’aziyar sa ga wadanda abin ya shafa tare da yi masu addu’a. Femi Adesina ne yayi wannan jawabi bayan faruwar abin. Shugaba Buhari ya mika ta’aziyar sa ga daukacin al’ummar Jihar Borno.

Rundunar Sojin Kasar dai ta tabbatar da wannan kuskure da aka samu wajen aiki ta bakin Birgediya-Janar Rabe. Gwamnatin Tarayya dai tayi alkwarin agazawa wadanda abin ya shafa. 

Haka kuma shekaran jiya aka kai wani hari na kunar bakin wake a Masallacin Jami’ar UNIMAID ta Maiduguri da Asuba. An dai yi rashin sa’a mutane 5 sun rasu, ciki har da wani babban Farfesa na likitan dabbobi mai suna Aliyu Usman Mani.


[NAIJ Hausa]





No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...