Tuesday, January 24, 2017

An nada mace a matsayin Mataimakiyar Shugaban kasa


Adama Barrow ya zabi Fatoumata Tambajang Mataimakiyar Shugaban kasa




Sabon Shugaban kasar Gambia, Adama Barrow ya nada Fatoumata Tambajang a matsayin Mataimakiyar sa. Halifa Sallah, mai magana da bakin Barrow ya bayyana haka a wani taro da aka yi jiya da manema labarai a Garin Banjul.

Fatoumata tayi kokari wajen sasanta abokan gaban siyasa a zaben bara. H. Fatoumata tayi aiki a matsayin mai bada shawara a kan harkokin mata da yara lokacin Shugaban Kasa Dawda Jawara. Ta kuma rike Shugaban Majalisar matan Kasar. Fatoumata dai tana da kyautar lambar girma bayan hidimar da tayi wa Kasar.

Kwanan nan Yahaya Jammeh ya sauka da karfi da yaji bayan dakarun ECOWAS sun dura cikin Kasar. Ko shi dai Mataimakiyar sa a lokacin mace ce, wanda tayi murabus daga kujerar da rikicin siyasar nan ta taso.



[NAIJ Hausa]

No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...