Adama
Barrow ya zabi Fatoumata Tambajang Mataimakiyar Shugaban kasa
Sabon
Shugaban kasar Gambia, Adama Barrow ya nada Fatoumata Tambajang a matsayin Mataimakiyar
sa. Halifa Sallah, mai magana da bakin Barrow ya bayyana haka a wani taro da
aka yi jiya da manema labarai a Garin Banjul.
Fatoumata
tayi kokari wajen sasanta abokan gaban siyasa a zaben bara. H. Fatoumata tayi aiki
a matsayin mai bada shawara a kan harkokin mata da yara lokacin Shugaban Kasa Dawda
Jawara. Ta kuma rike Shugaban Majalisar matan Kasar. Fatoumata dai tana da
kyautar lambar girma bayan hidimar da tayi wa Kasar.
Kwanan
nan Yahaya Jammeh ya sauka da karfi da yaji bayan dakarun ECOWAS sun dura cikin
Kasar. Ko shi dai Mataimakiyar sa a lokacin mace ce, wanda tayi murabus daga
kujerar da rikicin siyasar nan ta taso.
[NAIJ Hausa]
No comments:
Post a Comment