Monday, January 9, 2017

Dan Gwamna ya fito takara; yace yanzu lokacin su ne


Dan tsohon Gwamnan Jihar Edo, Adams Oshiomole ya fito takara


Dr. Cyril Oshiomole yana neman kujerar Majalisa


Babban Dan tsohon Gwamnan yace yanzu lokaci ne na matasa






Dan tsohon Gwamnan Jihar Edo, Adams Oshiomole ya fito takarar Dan Majalisar Wakilai na Tarayyar Jihar. Dakta Cyril Oshiomole dai ya kama hanyar Mahaifin na sa wanda yayi shekaru 8 a matsayin Gwamnan Jihar Edo.

Dakta Cyril Oshiomole yace yanzu fa lokaci ne na samari ba tsofaffi ba. Babban Dan tsohon Gwamnan dai yana neman kujerar Mazabar Etsako a Majalisar Tarayya. Tsohon Dan Majalisar Yankin, Philip Shu’aibu ya dai zama Mataimakin Gwamnan Jihar.

Yanzu haka fastoci sun shiga Garuruwa irin su Auchi, Benin, Etsako da sauran su. Dakta Oshiomole dai ya fito ne a karkashin Jam’iyyar APC. Ana dai tunani Shugaba Buhari zai nada Adams Oshiomole wani matsayi bayan da aka gan su tare kwanaki a cikin Villa.


[NAIJ Hausa]


No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...