– An
harbi wata mata a Fadar Shugaban Kasa da kuskure
– Wani
Jami’in DSS ne ya saki linzamin bindigar sa bai sani ba
– Yanzu
haka an yi Asibitin Villa da ita
A jiya an samu tuntube a
Fadar Shugaban Kasa inda aka narkawa wata mata dalma ba da gan-gan ba. Yanzu
dai an kai wannan mata ma’aikaciyar Gidan Gwamnatin zuwa Asibiti domin samun
lafiya.
Wannan tsautsayi ya faru ne
Jiya Laraba bayan da wani Jami’in Hukumar DSS ya saki bakin linzamin bindigar
sa bai sani ba. Jami’in yana kokarin ajiye bindigar sa a Kasa kenan kawai sai
ya saki harsahi a cikin wannan mata.
Wanda abin ya faru a gaban
idon sa yace an yi wa wannan mata rauni a ciki da cinya da dalma. Yanzu haka
dai tana Asibitin Gidan Gwamnatin da ke Fadar Shugaban Kasa inda ake kula da
raunin.
Idan ba a manta ba dai
kasafin kudin bana na sama da Naira Tiriliyan 7, Fadar Shugaban Kasa za ta
kashe sama da makudan kudi wajen sayen cokula cin abinci. Wasu dai na ganin ana
facakali da kudin al’umma a Kasar
No comments:
Post a Comment