Friday, January 13, 2017

Sanatocin APC 39 da suka tunbuke Sanata Ndume


– Sanatocin APC sun tsige Ali Ndume daga Shugaban masu rinjaye a Majalisar


– Sanatoci 39 na APC cikin 63 suka sa hannu wajen tunbuke Ndume




Sanatoci 39 cikin 63 na Jam’iyyar APC da ake da su a Majalisar Dattawa suka saka hannu wajen tsige Ali Ndume daga kujerar sa. Tuni kuwa dai har an nada Sanata Ahmed Lawan a matsayin wanda zai maye gurbin na sa.

A wani kudirin da ke nuna rashin amanna da Sanata Ndume, Shugaban Majalisar Dattawar, Bukola Saraki, ya karanta takardar da ‘Ya yan APC suka aiko na cewa sun cire Ndume. Sai dai tuni ya wanke kan sa, yace ba shi ya kashe zomon ba, rataya kurum aka ba shi.

Sanatocin da suka cire Ndume dai sun hada da: Dino Melaye, Sulaiman Nazif, Mustafa Bukar, Barau Jibrin, Rabiu Kwankwaso, Usman Nafada, Baba Garbai, Kabir Marafa,Tijjani Kaura, Sulaiman Hunkunyi, Shehu Sani, Ubale Shitu, Aliyu Abdullahi, Umaru Kurfi, Abubakar Yusuf, Kabir Gaya, Shaba Lafiagi, Ibrahim Gobir, Isa Misau.

Saura sun hada da Ali Wakili, Ahmed Bakura, Ahmed Lawan, David Ummaru, Danjuma Goje, Binta Masi Garba dsr. Shi dai Sanata Ahmed Lawan yace ba don yana son kujerar sai hau ba. 




[NAIJ Hausa]

No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...