Thursday, January 19, 2017

Rikicin Kudancin Kaduna: Saura kiris a kashe Sarki


Sarkin Jama’a ya tsallake rijiya da baya bayan an kai masa hari


Fulani Makiyaya suka kai ma Sarkin hari


Allah yayi da sauran kwanan Sarkin na Kafanchan




A jiya ne Sarkin Kafanchan ya tsallake rijiya da baya bayan da Fulani Makiyaya suka kawo masa hari. Saura kiris dai maharan su ga bayan Sarkin Jama’an. Allah dai ya tsaga da rabon kwanan mai martaba a gaba.

Duk da dai Sarkin ya tsira da kyar, Maharan sun yi kaca-kaca da motocin da ke tawagar sa. An dai dagargaza motoci uku da ke takewa Mai martaba Sarkin baya a harin da aka kai. Maharan dai sun tare Sarkin ne yayi da yake dawowa daga Garin na Kafanchan.

Idan ba a manta ba Sarkin da sauran takwarorin sa na Jihar, sun gana game da batun tsaron Yankin da Mai girma Gwamna Malam Naisru El-Rufa’i a Garin Kaduna. Tuni dai dama Gwamnan ya kafa dokar hana fita a Yankin. Shi ma dai Ciroman Jama’a, Alhaji Kabiru Tanko da kyar ya sha.

Dama dai jiya wani Dan Majalisar da ke wakiltar Karamar Hukumar Kaura da ke cikin Yankin Kudancin Kaduna, Honarabul Gideon Gwani ya koka da yadda lamarin tsaro ya tabarbare a Yankin. Dan Majalisar yace Mutanen suna cikin matsala don kullum cikin kai masu hari ake.


[NAIJ Hausa]

No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...