Thursday, January 12, 2017

Najeriya ta karbe matsayin ta a Afrika



Najeriya ta koma ta 1 ta a jerin masu hako man fetur


Kasar Najeriya ta doke Angola a Afrika


Najeriya ta fita daga wannan matsayin tun a bara



Najeriya ta komo matsayin ta na farko a jerin Kasashen da ke hako man fetur a Nahiyar Afrika. Najeriya dai ta doke Kasar Angola bayan Kasar ta dauki watanni kusan 7 suna matsayin na farko a Nahiyar gaba daya.

A bara ta kai Angola tana hako da gangar mai miliyan 1.7 yayin da Najeriya ba ta hako abin da ya wuce 1.5. Wannan dai zai bayu ne ga matsalolin da aka rika samu daga Tsagerun Neja-Delta. A watan Disamban da ta wuce ne dai harsashen Kungiyar OPEC ya nuna cewa Najeriya ta kerewa Kasar Angola da kusan ganga 100,000.

Kungiyar OPEC ta bayyana cewa Najeriya ta zarce Angola bayan yarjejeniyar da aka yi na rage yawan man da ake hakowa a kowace Kasa. Wannan zai sa Kasar Angola da rage ganga 78,000 a kowace rana.

Kungiyar OPEC ta Kasashen Duniya masu fitar da man fetur ta bayyana Dan Najeriyar nan, Mohammed Barkindo a matsayin Gwarzon wannan shekarar. Mohammed Barkindo wanda shine Sakataren Kungiyar yayi namijin kokari wajen tashin farashin gangar mai a Duniya daga Dala $30 zuwa sama da Dala $50 a kasuwannin Duniya.



[NAIJ Hausa]

No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...