Thursday, January 26, 2017

Wai da gaske ne Osinbajo zai sauka?


Ofishin Mataimakin shugaban kasa ya karyata rade-radin cewa ana nema a tursasa Osinbajo yayi murabus


Mai ba Shugaban Kasa shawara kan harkokin siyasa yayi bayani


Sanata Ojudu yace wannan karyar banza ce





Ana ta yada rade-radin cewa Mataimakin shugaban kasa, Farfesa Yemi Osinbajo na shirin ajiye aiki bayan matsin lamba da yake samu. Fadar Shugaban Kasa dai ta yi wuf ta maida martani ga masu yada jita-jitar inda tace sam karyar banza ce ba gaskiya ba.

Mai ba Shugaban kasa shawara a game da harkokin siyasa, Sanata Babafemi Ojudu yayi jawabi daga Fadar Shugaban kasar. Sanata Ojudu ya bayyanawa Jaridar Punch cewa rade-radun da ke yawo ba gaskiya bane. Rahotanni sun bayyana a baya cewa wasu Gwamnoni na neman tursasa Osinbajo yayi murabus.

Sanata Ojudu yace babu kanshin gaskiya ko na sisin kwabo a cikin maganar. Yanzu haka dai Mataimakin Shugaban kasar ne ke rike da Kasar a matsayin mukaddashi. Kuma yana kan aiki ba dare ba rana.



[NAIJ Hausa]

No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...