Friday, January 6, 2017

Ba mu san inda Shekau yake ba-Inji Sojin Najeriya


– Sojojin Najeriya sun ce ba su san inda Abubakar Shekau yake ba


– Wani Kwamandan Sojin yake cewa maganar ace Shekau na Kala-Balge duk rade-radi ne


– Sojojin Kasar dai sun share Dajin Sambisa, sun ce Boko Haram kuma har abada




Rundunar Sojin Najeriya ta bayyana cewa ba ta san inda Shugaban Kungiyar Boko Haram din, Abubakar Shekau ya shige ba. Rundunar Sojin Kasar suka ce maganar cewa Shekau din ya tsere zuwa Kala-Balge ko wani wuri can duk rade-radi ne wanda ba wanda zai iya tabbatarwa.

Manjo Janar Irabor Lucky wand shine Shugaban Rundunar Operation Lafiya Dole yace sun rasa gane inda Shekau din ya shige. Kwamandan yace da zai gan sa, da ya kuwa damke sa. Kwamandan dai ya kara tabbatar da cewa an gama da Boko Haram a Yankin.

Sojojin Kasar dai sun kira Jama’a su bada na su gudumuwar domin samun zaman lafiya a Yankin Kasar. Ana dai cigaba da kama ‘Yan Boko Haram da dama a cikin Kasar, sai dai har yanzu babu labarin Shekau.

Mai taimakawa shugaban kasar, Muhammadu Buhari wajen yada labarai Mista Femi Adesina, yace Yakin Boko Haram ba na taho-mu-gwabza bane, hakan ya hana a kama Shugaban Kungiyar Abubakar Shekau tuni.






[NAIJ Hausa]

No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...