Saturday, December 24, 2016

Hudubar Juma’a daga Mimbarin ITN-Zaria


‘Riko da Sunnah II-Daga Bakin Imam Ustaz Dr. Sa’eed Yunus





Assalamu Alaikum wa Rahmatul Lah,
Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah SWT wanda ya aiko Manzon Sa da shiriya da Addini na gaskiya da ya rinjaye sauran Addinai. Ina gode masa, ina jinjina masa, ina tuba gare sa, ina neman gafarar sa, ina shaidawa cewa shi kadai yake ba shi da wani abokin tarayya. Ya tsarkaka da duk abin da Azzalumai suke fada. Shaidar da za tayi amfani Ranar da ‘Ya ‘ya da dukiya ba su da amfani.

Ina shaidawa cewa Annabi Muhammadu, bawa ne kuma Manzom Allah. Allah ya aiko sa domin yayi bushara da kuma gargadi. Annabi SAW lallai ya isar da sako. Allah kuma ya daga darajar sa da matsayin sa. Sannan kuma Allah ya gusar da kuskure gare sa. Allah ya saka kaskanci da wulakanci ga wadanda suka sabawa Manzon sa. Lallai mu Masoya Manzon Allah SAW ne, kuma muna rokon Allah ya tabbatar da mu a kan haka. Allah ka dada tsira ga Farin Jakada; Annabi Muhammadu SAW da Sahaban sa da iyalan sa da sauran wadanda suka bi tafarkin sa zuwa Ranar karshe.

Bayan Haka:
Yayin da fitina suka watsu a Doran Kasa cikin Al’umma, ana ta Hudubobi, gaskiya ta hadu da karya. Ana cikin rudu Jama’a! Mafita day ace; A ji tsoron Allah. Tsoron Allah kadai zai haska hanya. Duk wanda Allah ya azurta da tsoron sa, ya samu gam-da-ka-tar.

Daga cikin masu batar da mutane, za ka ji su da zakin baki. Allah dai yace idan har ku ka ji tsoron sa, zai gafarta maku zunuban ku, ya kuma azurta ku arziki mai yawa. Ubangiji kuma yace Idan kun ji tsoron sa, zai ba ku mafita, domin Allah mai falala ne. ‘Yan uwa tsoron Allah babbar kyauta ce, duk wanda Allah ya azurta da tsoron sa, ya sami kubuta daga hanyar Shaidn. Allah ne yace idan ku ka yi Imani ku ka ji tsoro na, Allah zai ribanye masu haske ya kuma gafarta masu, domin Shi mai Gafara ne kuma mai Rahama.

Imam Yahaya dan Yahaya yake cewa tsayuwa tsayin daka ya fi tafiya Jihadi. Abu Ubayda Dan Salma kuwa yake cewa wadanda suka rike Sunnah tamkar sun rike garwashi ne. Yanzu kuwa kana iya cewa tamkar a doke ka da takobi; dubi yadda ake wulakanci a yau, Musulmai suna cikin kaskanci; sun kawo abubuwan da ba su cikin karantarwar Addinin Manzon Allah; sun hada gaskiya da karua, Sunnah ta zama bidi’a. Yaushe ne za mu fita daga wannan rudu? Yaushe ne za mu banbamce tsakanin Makiyi na fili da Masoyi domin Allah.

‘Yanuwa ta ya za muyi hidima ga Addinin Allah? Ta ya za mu kare Sunnar Ma’aiki? ‘Yan uwa masu rubutu a Jaridu, ta ya za ku yi tallar Addinin mu, kuma a san cewa abin da ba karantarwar SAW ba, ya sabawa Addinin mu. Ta ya za kuyi wa mutane bayani har ya zama ba za a samu ragonta ba ko wuce gona da iri? Ina makarantun Islamiyyun mu? Ina makarantun Hardar Al-Qur’ani? Ya ku dalibai na Sunnah, idan har da gaske ku ke, mu ga Sunnah a Kasa. Ya kai wanda kake Musulmi, ka nunawa wanda ba Musulmi ba cewa lallai Addinin Musulunci addini ne na gaskiya. ‘Yanuwa masu girma ku sani cewa idan kun yi haka, Allah zai cika maku alkawarin da yayi maku. Gare Sa ne ake samun nasara da kuma dacewa, Allah ka bami nasara ka sa mu dace.




Huduba ta biyu, bayan godiya ga Allah; wanda ya rarrabe tsakanin hanya ta gaskiya da ta karya, wanda ya aiko Manzani na sa masu yawa masu gargadi don ka da wasu su ce a Ranar Lahira Allah bai aiko da Manzo ba. Ina shaidawa Allah shi kadai yake ba shi da abokin tarayya, ina shaidawa cewa Annabi Muhammadu SAW Bawan Allah ne kuma Manzon sa ne. Hakanan Sahaban sa da Iyalan sa, tsira da amincin Allah ya kara tabbata a gare su.

Bayan Haka:

‘Yan uwa mu ji tsoron Allah, mu rike Sunnar Manzon Allah SAW, mu sani cewa lallai Allah ya zabe mu ne, don haka ne ya saka mu cikin al’ummar sa. Kuma mu sani cewa mafi alherin haske shi ne Al-Kur’ani, kuma Mafificiyar shiriya ita ce shiriyar Annabi Muhammad SAW kuma mafi sharrin al’amari shine wanda aka kirkira aka danganta shi da Annabi Muhammad SAW, sannan kuma duk abin da aka kirkira a Addini Bidi’a ne, kuma duk Bidi’a bata ce.

‘Yanuwa masu girma, daga cikin Rahamar Allah ga abayin sa, Allah ya saukar da littafi na Al-Kur’ani; wanda ya kasance haske ne a kowane zamani, kuma Allah ya azurta wasu mutane masu tsayuwar daka suna karantar da Jama’a da kokarin ganin mutane a kan tafarkin Manzon Allah. ‘Yan uwa ka da ku manta idan kiyama ta tashi, Allah zai kira wasu Mala’iku yace masu: Ga wasu bayi na sun canza bayan tafiyar Manzon Allah SAW. Annabi yana kokarin kiran su, sai a fada masa cewa ai sun canza, sun canza…Allah ka da ka sa mu cikin wadannan mutane. ‘Yan uwa masu girma, mu sani cewa hakki ne a kawunan mu gaba daya duk wani Musulmi da yake rayuwa a doron Kasa, gwargwadon abin da zai iya, ya san cewa wajibi ne a kan sa ya raya Sunnar Manzon Allah SAW, ya taimaki Musulmai, ya karantar da su abin da ya sani; hakan ne hanyar shiga Aljanna. ‘Yan uwa muna da wata hanya ta shiga Addini ne ba ta Annabi Muhammad Al-Mustafa ba? Ba mu da hanyar da ta wuce ta sa da ta Sahabbai wanda sune shiryayyun wannan al’umma. Ya kai me neman kubuta, ina kiran ka da riko da Sunnah, ka yi biyayya da karantarwar Manzon Allah da ta Sahabbai. Ina gargadin ka da ruduwa da wasu mutane da suke fitar da mutane da harshen su; da Hadisan suna karya, da karatun san a Kur’ani. Za su kasance masu zakin baki, amma suna adawa ne da Al-Kur’ani, ka sani cewa gaskiya ba ta bukatar ado. Gaskiya kuma ba ta bukatar yawa, sai dai hujja da dalili. Allah yana fada mana cewa idan ka bi yawan mutane za su batar da kai daga hanyar Allah.

‘Yan uwa a yau muna fama da kalubale a matsayin mu na Musulmai masu nema mu raya Sunnar Ma’aiki SAW, saboda wasu sun shigar da wasu abubuwa cikin Sunnar Ma’aiki. Wadannan mutane suna neman daukaka, suna nema a san su a Duniya. Daraja fa a hannun Allah take. Allah ne ya fitar da Annabi Musa AS daga Gidan kaskanci zuwa Gidan Fir’auna. Allah ne ya raya sa har ya zama abin da zai zama a Gidan Fir’auna. Allah ne ya fitar da Manzon sa SAW a Maraya. Allah ne kuma ya fitar da Annabin sa Yusufu AS daga kasakanci. Ya kai mai tsoron Allah, ina kiran ka, ka yarda Allah ne ke ba da daraja ba yawan mutane ba. Ka tuna cewa wata rana za ka wayi gari kai daya a kabari.

‘Yan uwa mu yi kokari mu cike duk wata gaba a karantar da mutane Sunnah cikin kwanciyar hankali; babu zagi, ko zolaya ko habaici. ‘Yan uwa mu nunawa Allah cewa mu mutanen kirki ne, domin wallahi idan har muka nunawa mutane cewa haka, Alhali ba hakan bane, mun shiga wani hali.

Lallai Kasar mu tana bukatar Addu’a, akwai bukatar a karantar da mutane Sunnah. Rashin sanin Sunnah ce ta sa mutane suke tafiya a baude. Dama Manzon Allah SAW yace idan karshen zamani ya zo, mutane za su kasance cikin rudu sai wanda suka yi riko da Sunnah. Babban al’amari shine tsoron Allah.
Sannan Huduba tana cewa muyi Salati ga Annabi Muhammad SAW. Addu’a.





Muhammad Malumfashi yayi aikin wannan huduba daga Masallacin I.T.N-Zaria.
Muhammadmalumfashi@gmail.com          

Twitter:@Ya_waliyyi

1 comment:

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...