Thursday, December 29, 2016

Ashe Makafi na satar amsar Jarrabawa



Jami’ar WAEC ya bayyana cewa ashe mafi yawanci makafi satar amsa suke yi lokacin jarrabawa


Misis Francis Iweha-Onukwu tace rashin kintsi ke jawo haka


An kira Gwamnati ta kara karfi wajen harkar ilmi



Wata Jami’ar Jarrabawar WAEC ta Yammacin Afrika, ta bayyana cewa ashe mafi yawanci makafi masu rubuta jarrabwar, satar amsa suke yi domin su samu nasara. Jami’ar tace hakan na bayuwa ne saboda rashin shiryawa Jarrabawar da kyau.

An dai kira Gwamnatin Kasar ta kara karfi wajen harkar ilmi gaba daya. Hukumar Jarrabawar tace mafi yawanci, Makafi kan hada kai da ‘Yan uwan su ne suyi satar amsa a Jarrabawar. Jami’ar ta bayyana haka ne ga Manema labarai a jiya Laraba.

Hukumar Jarrabawar tace dalilin da ka jawo haka shine rashin shiri da kayan aiki da dalibai makafin suka rasa. An kira Gwamnati ta dage wajen harkar ilmin nakasassu da marasa karfi. Idan har Gwamnati ta sa karfi, ba shakka irin wannan dalibai suna da baiwar karatu, Inji ta.

Kwanan aka samu labarin wata mata da tayi shekaru 30 tana sana’ar abinci, da haka ta biyawa dan nan na ta kudin makaranta. Tun daga Ajin Nursery har ya kammala Sakandare inda ya rubuta jarrabawar WAEC. Wannan yaro dai yace uwar sa ce uban sa.

[NAIJ Hausa]





No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...