– Hukumar ‘Yan Sanda tace za ta dauko Turawa domin su tantance muryar Gwamna Wike
– Ana dai ta binciken abin da ya wakana na magudi a
Jihar Rivers
– Hukumar ‘Yan Sanda tace za tayi iyaka kokarin ta wajen
ganin an yi gaskiya
Jami’an Tsaro sun nemi
taimakon wasu kwararru daga Kasar waje domin su taya su binciken sautin da aka samu na
Gwamnan Jihar Rivers, Nyesom Wike inda yake kokarin murde zabe da ma alwashin kashe wani
Jami’in zaben a wayar tarho.
Cikin makon nan da ya gabata
ne Sufeta na ‘Yan Sanda, Ibrahim K. Idris ya bayyana haka. Sufetan ya koka da
rashin Jami’an san a ‘Yan Sanda a wajen zaben, yace hakan ba zai kara faruwa a
Kasar nan ba.
Dama can mun rahoto cewa
Hukumar ‘Yan Sanda na Kasar ta nada kwamitin da ke dauke da wani kwararre a
harkar
irin wannan binciken.
Za a gabatar da wannan aiki cikin wata guda, kuma a fitar da sakamako.
Sai dai Gwamna Wike yace can su ji da shi. Hukumar DSS ma
ta zarge sa da yunkurin tada zaune-tsaye a Birnin Tarayyar Abuja. Gwamnan dai
yace Jami’an tsaron ba su yi masa adalci kuma suna kokarin kare Ministan
Buhari, Rotimi Amaechi.
No comments:
Post a Comment