– Da
alamu kwanakin Babachir David Lawal a matsayin Sakataren Gwamnati sun zo karshe
– Akwai
yiwuwar Shugaba Buhari ya fara neman wadanda za sum aye gurbin sa
– Ana
zargin Sakataren Gwamnatin Kasar da wasu laifuffuka
Rahotanni na nuna cewa
Shugaba Buhari ya fara cigiyar Sabon Sakataren gwamnatin tarayya wanda zai maye
gurbin Babachir David Lawal. Majalisar Dattawa dai ta jefawa Mista Babachir din
kashi dumu-dumu a jika.
Jaridar Daily Post ce dai ta
kawo wannan rahoto. Shugaban Kasar dai ya fara neman wanda zai zama sabon
Sakataren Gwamnati. A Ranar Larabar nan wani da ke Fadar Shugaban Kasa ya
bayyana cewa an fara bidar sabon Sakatare.
Majiyar ta nuna cewa cikin
wadanda ake sa rai su canji Sakataren, akwai Audu Ogbeh wanda shine Ministan
noma na Kasar. Akwai kuma wasu tsofaffin ma’aikatan Gwamnati da ake tuntuba
domin su canji Babachir din.
Ko a shekaran jiya dai Wani Tsohon
Shugaban Majalisar Dattawan Kasar nan, Adolphus Wabara, ya kira Sakataren gwamnatin
tarayya, Babachir David Lawal ya sauka daga matsayin sa saboda tarin zargin da ke kan
sa.
A biyo mu a
shafin mu na NaijComHausa
No comments:
Post a Comment