– Jami’ar ABU ta Zaria za ta gina Makarantar koyon kasuwanci
– Majalisar Jami’ar ta bada damar ayi wannan aiki
– Akwai irin wannan Makarantar tuni a Legas
Jami’ar Ahmadu Bello watau
ABU Zaria za
ta bude Makarantar koyon kasuwanci. Majalisar Jami’ar ta amince a bude wannan
Makaranta kamar yadda Shugaban Jami’ar, Farfesa Ibrahim Garba ya bayyana.
Farfesa Ibrahim Garba ne yayi wannan bayani a Jiya wajen
bikin gina wani Dakin taro mai daukar mutane 300 a Jami’ar. Kungiyar ICAN ta
kwarararrun Akawu na Kasar ce za ta gina wannan dakin karatu.
Idan har an bude Makarantar Koyon kasuwancin, za a rika
koyar da Ilmin Tattali da akawu da Ilmin kasuwanci har da ma Ilmin Banki na
Musulunci da sauran su. Farfesa Garba yace Makarantar za ta rika bada shaidar
Digirgir da Digir-digir da ma Diploma. Dama can akwai irin wannan Makaranta a
Jihar Legas.
Kwanakin baya Jami’ar ta yaye dalibai masu digiri guda 11,
731. Kamar yadda muka samu labari akwai guda 2, 697 masu shaidar Digiri na
biyu, sannan kuma guda 289 sun kammala karatun Digiri na uku. Akwai kusan 50
masu Digiri mai makin farko watau first
class. Jami’ar Ahmadu Bello dai ita ce ta farko a Arewacin Najeriya.
[NAIJ Hausa]
No comments:
Post a Comment