Sunday, December 11, 2016

Mu ba barayi bane-Sanatoci sun yi kaca-kaca da Buhari

Sanatocin Kasar nan sun ce akwai matsala wajen yaki da rashawar da Shugaba Buhari yake yi

 


Sanatocin sun ce karya ake yi da ake cewa su suka fi sata a Najeriya

 


Sanotocin sun ce akwai wadanda Buhari ya kamata ya sanyawa ido ba su ba

 





Sanatocin Kasar nan sun ce akwai matsala wajen Yaki da cin hanci da rashawa da Shugaban Kasa Muhammadu Buhari yake yi. Sanatocin sun ce gaba daya Shugaba Buhari ya sa ido kan wadanda ba su ke sata ba. 

Wani taron Sanatocin Kasar ne suka fadawa Jaridar Premium Times haka. Sanotocin suka ce Masu aikin Gwamnati Buhari ya kamata ya bi, ba ‘yan siyasan Kasar ba. Sanatocin sun yi wani Taron ‘Yan Majalisa ne a Kasar Afrika ta Kudu.

Sanotocin sun ce aikin ma’aikatan Gwamnati ne su tabbatar da an aiwatar da kasafin kudin Kasar, don haka su ya kamata a rika bincike ba ‘Yan siyasa ba. Wasu Sanatocin sun musanya batun cewa sune suka fi kowa sata a Kasar, suka ce ba haka abin yake ba. 

Sanata Theodore Orji mai wakiltar bangaren Jihar Abia yace a baya ya samu labarin cewa ana samun kudi a Majalisar. Sai da ya zo, sai ya ga ba haka abin yake ba.


[NAIJ Hausa]

No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...