– Kungiyar CAN tace har yanzu ba ta
canza matsay ba game da Gwamnatin Jihar Kaduna
– Gwamnatin Jihar ta kawo kudirin
takaita wa’azi a Jihar
– Kungiyar
Kiristoci sun nanata cewa ba su fa yarda ba
Gwamnatin
Jihar Kaduna ta kawo wani kudiri ga Majalisar Jihar da zai sa Gwamnati ta rika
lura da sha’anin wa’azi a fadin Kasar. Kungiyar dai sun kara nanata matsayar su
na cewa ba su yarda da wannan kudiri ba.
A
baya ne dai Gwamnan ya tado da wannan doka wanda dama can tafi shekaru 30 a
cikin dokokin Jihar. Kungiyar CAN da ma ta FPN sun maka Gwamnan a Kotu saboda
yunkurin farfado da wannan doka a Jihar.
Sakataren
CAN na Jihar Kaduna ya bayyanawa manema labarai a wata hira cewa har yanzu ba
su amice da yunkurin takaita wa’azi ba a Jihar. CAN tace akwai lauje a cikin
wannan nadi. Ibrahim Sunday yace an
shiga hakkin su. Yanzu haka dai an kai karar Gwamnan a gaban Alkali Hajarah
Gwadah a Babban Kotun Jihar.
Wancan
mako ne kuma dai ya bayyana cewa daga yanzu babu wani tattaki ko gangamin da ya
sabawa doka a Jihar. Gwamnatin tayi wannan ne domin kawo karshen lamarin ‘Yan Kungiyar IMN na Shi’a a Jihar Kaduna.
[NAIJ Hausa]
No comments:
Post a Comment