Friday, December 23, 2016

Kungiyar CAN ta kara nuna El-Rufai da 'dan yatsa


– Kungiyar CAN tace har yanzu ba ta canza matsay ba game da Gwamnatin Jihar Kaduna


– Gwamnatin Jihar ta kawo kudirin takaita wa’azi a Jihar


Kungiyar Kiristoci sun nanata cewa ba su fa yarda ba




Gwamnatin Jihar Kaduna ta kawo wani kudiri ga Majalisar Jihar da zai sa Gwamnati ta rika lura da sha’anin wa’azi a fadin Kasar. Kungiyar dai sun kara nanata matsayar su na cewa ba su yarda da wannan kudiri ba.

A baya ne dai Gwamnan ya tado da wannan doka wanda dama can tafi shekaru 30 a cikin dokokin Jihar. Kungiyar CAN da ma ta FPN sun maka Gwamnan a Kotu saboda yunkurin farfado da wannan doka a Jihar.

Sakataren CAN na Jihar Kaduna ya bayyanawa manema labarai a wata hira cewa har yanzu ba su amice da yunkurin takaita wa’azi ba a Jihar. CAN tace akwai lauje a cikin wannan  nadi. Ibrahim Sunday yace an shiga hakkin su. Yanzu haka dai an kai karar Gwamnan a gaban Alkali Hajarah Gwadah a Babban Kotun Jihar.

Wancan mako ne kuma dai ya bayyana cewa daga yanzu babu wani tattaki ko gangamin da ya sabawa doka a Jihar. Gwamnatin tayi wannan ne domin kawo karshen lamarin ‘Yan  Kungiyar IMN na Shi’a a Jihar Kaduna.


[NAIJ Hausa]

No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...