Thursday, December 22, 2016

An so a kai hari Gidan Shugaban MURIC



– Shugaban Kungiyar MURIC ta Musulmai ya tsallake rijiya da baya-da baya


– Farfesa Akintola ya bayyana cewa wasu na nema su ga bayan sa


Sai dai ba wannan ba ne karo na farko ba



Darektan Kungiyar nan ta MURIC ta Musulmai ya bayyana cewa wasu mutane sun yi yunkurin ganin bayan sa. Farfesa Akintola yace wasu mutane ne suka bi sa har gida a Ranar Lahadin nan da ta wuce.

An dai san Ishaq Akintola da Kungiyar MURIC da tsoma baki cikin lamarin harkar Kasa, musamman wanda zai shafi Musulmai. Farfesa Akintola yace wasu mutane hudu suka dura gidan sa da sunan suna neman sa.

Malam Yakeen Williams da Shefiu Ayorinde suka rubuta jawabi a madadin Darektan Kungiyar ta MURIC. Suka bayyana duka abin da ya wakana. An yada wannan jawabi a kafafen yada labarai na zamani. Ba dai yau aka fara kai wa Farfesan hari ba, ko shekaru uku da suka wuce, an samu irin wannan.

Mutane hudu ne dai suka tasan ma Gidan Farfesa Akintola a Ranar Lahadin nan, suna cikin Katuwar motar Toyota. Ko da suka isa sai suka ce suna neman Mai-Gidan ne domin su gayyace sa wani taro, da aka nemi su kira lambar sa idan da gaske ne, duk sai suka gagara. Ana dai zargin ana nema a sace ko ma kashe Farfesan ne. Kungiyar ta kira Jama’a su bi a hankali da kuma yi masa addu'a. 


Muhammad Malumfashi ya kawo wannan rahoto a Shafin labarai na NAIJ Hausa




No comments:

Post a Comment

Featured Post

Goron Juma'a: Falalolin Ranar Juma'a a Musulunci

Manyan faloli 3 na Ranar Juma'a mai albarka  A yau dai ta ke Ranar Juma'a wanda ba shakka ke da falala Musulmai sun dauk...